RASHIN HAIHUW
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.W.FHome of gorgeous,intelligent and experts writers, we are the best among the rest
Written by fateema Adamu Gamawa
Fateegamawah
Wai yane naga commentes yafara kasa ne
Page 23
A hankali na bude idona
a kasa na ganni kwance
Tashi nayi hade da karewa falon kallo tunani na shiga yi shin mai yafaru naganni a nan ganin nakasa tunawa ne yasa na daga kafata daniyyar intafi dakina
Wani abu na taka kamar jini tunani na Shiga yi ina kuma na hadu da jini
Cak na tsaya sakamakon tunani abinda yafaru Dana yi nan gumi yafara keto min jikina yafara rawa innalillahi wa inna ilahir raju una shi kawai nake maimaitawa falon nashiga zagayewa
Tsabar tashin duk lakar jikin mutuwa tayi tsayiwar ma gagarata tayi zuciyata kuwa sai bugawa take da tsananin karfi haka na dafe kirjina kamar raina Zai fita ina zaune a wurin naji a kiran sallah ni a tunina Nina asuba ce ake kira, agogo na kalla ga mamakina sai na ga ya nunamin karfe bakwai ahhh toh sallah yaushe ake yi yanzu karfe bakwai gabana ne yafadi kaddai yaron Rahma ne ya mutu za a sallah ceshi nashiga ukuna
Kat kat kat jikina ya Shiga rawa, bugun zuciyata kuwa sai karuwa yake nanfa tari ya sarke ni a wurin
aman jini nafara can kuma idona yafara rufewa na fara ganin duhu but am not ready for dat ina so na San yaron Rahma yamutu ko bai mutu ba amma ina inaji haka duhu ya mamamye ni "Rahma Rahma Rahma .........
*******
Jinayi an watsa min ruwa mai tsananin sanyi a firgice na tashi ina cewa " Rahma RahmaRahma........"
Wani mari naji akan fuskata tas kafin nafarkon ya gama register a brain dina nasa
ke jin wani tuni na dawo hayyacina domin wannan yamafi na farkonTashi nayi tsaye duk da jirin sake dibana dago kaina nayi domin naga Wanda yamin wannan aika aikar wazan gani
ANTY LUBA
Ido na zaro ina kallonta ina tunanin mai kuma ya kawo Anty luba Dubai
toh kodai mun dawo 9ja ne amma Dana kalli falon saina gane har yanzu dai muna dubai , kenan zuwatayi tab nabano masifa kan masifa yau ni Ahlam INA ganin RAYUWA
Katse ni tayi daga tunanin dana Lula ta hanyar cewa "toh bakar makira, muguwa yar gidan Azzalumai burinki baki cikaba domin cikin bai zube ba "
Wata irin ajiyar zuciya mai nauyi na sauke nan naji zuciyata tadan fara sanyi Allah na godemaka dan idan hameed ya sake ni bansan makumataba rayuwata bata da wani anfani in babu shi nasan dayawa zasuji haushina idan suka ji abinda nayi amma da hameed ya sakeni na kwammace ayita yankan naman jikina kullum domin komai yayi min nasan ba a hayyacinsa yake ba
Jirin Dana ke jine yake kokarin kadani Sauri nayi na tsugunna tareda fashewa da wani kuka Wanda tun jiya nake so nayi amma yaki zuwa sai yau
Salati naji Anty luba tanayi tana tafa hannu hadi dacewa
"Yau ni lubabatu naga ikon Allah wato dan nace miki cikin bai zube ba shine harda wani kuka kai wannan ya' kin cika shedaniya toh ta Allah bataki ba kuma kina cikin gidan nan za'a haifo mana jariri "
Tashi nayi na barmata wurin na wuce dakina domin idan na tsaya zuciya zata iya tunzurani nayi abinda zanzo INA dana sani nakasance mai tsananin hakuri amma fa idan raina ya baci bani da kyau ko kadan
dan akwai lokacin da muna primary wata yarinya kullum saita tsokane ni, sai ta tara yara suyi tabina a baya suna tsokanata aikuwa ranar datakini bangu uhum doka namata na fitar hankali ko malamai kasa karbanta sukai domin wani karfi ne yan zo min
saida naga bata numfashi sannan na barta faga nan kowa tsaorona take domin su duk sunsha Aljanu gareni ko malami daina suka sukayi itakuw a wannan yarinyar Allah ne kawai yasa dasauran kwanan ta domin dakyar ta rayu wannan ne yasa Abbu na yahanani fada koda wasa Yakuma ce duk ranar da nakumayin fada tofa shidai ba Abbu na bane saidai na nemai wani
Amma lallai watarana sainayiwa Anty lubama haka
****************Waishin ya zaman Ahlam da Anty lubsy Zai kasance
Insha Allahu zuwa dare Zaki sake jina
Fateegamawah taku ce
![](https://img.wattpad.com/cover/181898347-288-k23306.jpg)
YOU ARE READING
RASHIN HAIHUWA
Non-FictionAhlam baiwar Allah ce wanda bata taba haihuwa ba har tayi shekara goma da aure gashi yan uwan miji sun takura mata har sukasa yayi aure cikin ikon Allah kuwa ita matar daya auran ta haihu sai take tama gori da rashin mutumci