12.

463 71 25
                                    

I just want to say a big thank you to all of you who've been following this story despite how inconsistent I am. I really appreciate you guys. Thank you so much Allah ya saka da alkhairi Ameen. Sannan kuma ku sakani a addu'arku Allah ya sa na rinka updating regularly Ameen😅.

"I met someone" fadin Mu'azzam kenan bayan sun fara session din nasu na ranar shi da Doctor Brown.

Ta kalleshi cikin mamaki. Hakan ya saka shi murmushi. Cikin harshen turanci yace "Nasani Doc. Ni ma ban taba tsammanin hakan zai faru da ni da  wuri ba."

"An samu cigaba kenan" cewar Doctor Brown. Ta danyi rubutu a wata takarda tana murmushi. "Bani labari. A ina kuka hadu? Kuma a wani mataki alakar ku take?"

Ya sake nutsewa cikin lallausar kujerar da ke opishin Doctor Brown din. Zuwan nashi jefi-jefi ne. Wasu lokutan ma sai sakatariyarta ta tura mishi sako don ta tuna mishi da appointment din nashi. Wani lokacin yaje wani lokacin kuma yayi harkokin gabansa. To yanayin da ya samu kansa a watanni uku da suka wuce ya sa shi fara zuwa wajenta akai-akai.

Itama Doctor Brown din ta lura da canjin data gani a tattare da shi kawai dai batayi magana bane tafiso ta ji daga gareshi. Gashi kuma yanzu ya fada mata da bakinshi.

Idonshi ya yawata a opishin nata madaidaici wanda ta kayata shi da litattafai da kuma furanni masu sanyin kamshi. Ya fara bata labarin yanda Misriyya ta nemo lambar wayarsa a wajen Aishan Mujahid da yanda ba zato ba tsammani ta zame masa abokiyar hira.

Ta yi wa rayuwarsa shigan bazata. Don ko kadan bai saka ran zai sake ganinta ko ma yin magana da ita ba.

Sai ga shi duk lokacin da zai samu wani dan sarari zaka ganshi makale da waya.

"It feels like Najmah all over again" ya furta a hankali.

Yana lura da kallon da Amma take mishi kwana biyu. Tana so ta san me yake ciki. Tun da yake da ita kuma bai taba boye mata wani lamari game da shi ba sai wannan. Ya rasa meyasa ya kasa sanar da ita dukda yana ganin alamar kamar ta gane a idonta.

Fadawa Doctor Brown din ne yasa yaji kamar an rage mishi wani nauyi a kirjinshi. Kamar yana rike wani sirrin da yanzu ya samu damar furtawa.

"Hakan ya maka?"  Muryar Dr. Brown ta kutsa cikin kanshi.

Ya danyi shiru yana nazari kafin ya gyada kanshi a hankali.

"Kana hira da ita ne don kana sakata a gurbin Najmah ko kuma akwai wasu abubuwa a tattare da ita dayasa kake tare da ita wanda sam basu da alaka da Najmar?"

Ya dan yi shiru. "Bansaniba nima. Kawai tana saka ni dariya kuma tana sa na manta da dukkan wata damuwa ta. And she cares about me a lot" ya karashe yana tuno lokacin da ta tafi hutu Nigeria na tsawon sati biyu. Haka zata saka alarm ya tasheta karfe ukun dare wanda yayi daidai da karfe tara na dare agogon New York don tasan a lokacin ya dawo gida. A wannan lokacin tukin jirgin dayake na safe zuwa rana ne. Daga bakwai tayi to ya tashi amma kafin ya iso gida ya kikkimtsa yayi sallolinsa har taran tayi. Tunda ya sanar mata hakan kuwa sau daya shikenan koyaushe kamar agogo tara tanayi zai ga kiranta ya shigo. A lokacin yayi wanka yaci abinci har ya saka kayan bacci. Wasu lokutan yana makale da waya zaiyi bacci. Ita kuma sai ta tashi tayi sallar asuba.

Da ta dawo daga hutun nata haka ta ciko mishi jaka da kayan marmari irinsu kilishi, dambu, aya mai siga, gullisuwa da alawar madara.

Abun yayi masa dadi matuka don ko Amma dataje kwanakin baya in banda kilishi babu abun da ta kawo mishi wanda yake marmar. Haka yayi ta sanyawa Misriyyah albarka. Kuma a lokacin yaji zuciyarshi ta sanyaya da lamuranta.

MaktoubWhere stories live. Discover now