21.

675 106 94
                                    

Brace yourselves, this chapter is total chaos. You've been warned ⚠️ ❗❗❗.


21.

Kamar yadda sukayi, ranar asabar wajen karfe sha daya Fareeha ta shirya ta gangara gidansu Hafsatu. Dayake gidajen nasu yana da dan nisa, sai ta yanke shawarar ta hau abun hawa dukda cewa akwai hanya ta cikin layi, kawai dai bata son bin ta wajen ne saboda masu shaye-shaye sunyi yawa a ta wajen. Dama yaya unguwar tasu balle ka shige can cikin lungu?

Ko da ta isa, Hafsatu cikin murna ta tarbeta. Ta sameta tana aikin tsince shinkafa, don haka Fareehar ta zauna ta taya ta, suna yi suna hira. Bayan sun gama Hafsatu ta dora shinkafar a wuta; dama mamanta tayi miya da safe kafin ta wuce makaranta.

Sai da ta jira ta tuka tuwon suka ci sukayi sallah sannan suka nufi gidan lallen.

"Ni ban zaci gidan da nisa ba ai da mun hau napep" cewar Fareeha da ta ga tafiyar taki karewa.

Hafsatu ta yi 'yar dariya "Ke yanzu sai mu kashe kudi dan nan da can din? Ki bari dai ko a dawowa ne sai mu hau. Amma yanzu ai mun dan mike kafa."

Shiru kawai Fareeha tayi amma ba haka ta so ba. Ta dan ji sauki ma dayake garin babu rana sosai alamar zuwa yamma ko dare ruwan sama zai iya sauka.

Sun zo wucewa ta wani layi ne kawai Fareeha taji kamar an yafuto hijabin ta. Cikin sauri ta juya wanda yasa Hafsatun ita ma juyawa.

Wasu samari ne su biyu zaune akan dandamalin wani shagon saida provision suna 'yan zuke-zukensu. Su Fareeha ko lura basuyi dasu ba lokacin da suka zo wucewar.

Wanda ya yafuto tan ya dan daga mata gira "Ya ne? Ina zuwa?"

Wani kololon bakin ciki ne yazo ya tsaya a makogoranta lokacin da take kare masa kallo. Tsabar raini da hijabinta da mutuncinta amma shine zai yafuto ta saboda bashida kunya?

Ta bude baki da niyyar yi masa masifa taji Hafsatu ta ja hannunta tare da buga tsaki tana fadin "Dan iska kawai"

"Kinga abun da yasa nace mu hau abun hawa ko?" Fareeha ta fada bayan sun dan kara gaba da wajen.

Zuciyarta sai tafarfasa take saboda bacin rai. Rabon da a mata irin haka tun farkon tafiyar Ya Bilal rehab, kuma shi ma tun lokacin ba wanda ya kara tunkararta musamman ma da karatunta ya kankama a Kano, tunda ba ma wani ganinta suke ba balle su shiga sha'aninta.

Kuma tun da can dinma ba mai zuwa kusa da ita da kannenta saboda suna tsoron Ya Bilal din. Shine yanzu wannan ya samu damar jawo mata hijabi? Abun ya bata mata rai matuka

"Ki kyalesu da Allah. Saboda wadannan shashashun ne zamu fasa yawo a unguwa? Don sunga kaman ana jin tsoron su ne ai shiyasa suke ganin daman mutane. Amma in ka nuna musu baka tsoron su to shikenan. Ni kinga kowa ya tsare ni a hanya rashin mutunci nake kekketa masa."

Shiru Fareehan tayi kawai tana karanta Hasbiyallahu wa niimal wakeel a cikin zuciyarta don har yanzu tafarfasa takeyi.

Sun isa gidan lallen suka samu mutane da dama ana musu lalle wasu kuma ana musu kitso. Anan dai suka shaida wa Falmata akan lallai nanda sati uku masu zuwa zatazo ta yi wa Fareeha lallen ta na amarya, baki da ja. Falmata ta amince da hakan. Suka karbi lambar juna sukayi sallama suka dawo gidan su Hafsatu. Ko da zasu dawo Fareeha ta nace akan su hau Napep, haka Hafsatun ta hakura don taga ran kawar tata ya sosu sosai akan abun da ya faru dazun.

********

"How's the new place?"

Juyawa tayi tana yawata idonta a  dan falon nata wanda har yanzu bai amsa sunansa falo ba sai ma dai a kirasa da store saboda shirgin da aka jibge a ciki da kuma yanda komai yake a hargitse, hatta TV ma har yanzu yana kwali bata bude shi ba. Kujerun ma suna cikin ledarsu bata daye ba.

MaktoubМесто, где живут истории. Откройте их для себя