34.

1.2K 114 85
                                    


Hello my loves ❤.  A cigaba da hakuri da ni please and manage this chapter.




34.

"Yanzu Adda sai yaushe?"

Dariya ce ta kusa ta kubce mata a lokaci guda kuma taji kamar ta fashe da kuka.

A wasu 'yan shekaru a baya haka suka zauna a tsakar gidan nan ita da Maman Walid tana tambayar ta yaushe zata dawo idan ta koma makaranta. A lokacin kam tana da amsar da zata bata. Amma a halin yanzu, bata da shi.

Tun da Mu'azzam ya samu labarin yajin aikin da aka shiga na kungiyar malamai ta jami'o'i wato ASUU, yace to tayi maza-maza ta hada nata ya nata ta taho. An yi rashin sa'a ne ma ya cinye duk hutun sa na shekara a dalilin sintirin da yayi tayi a tsakani amma babu makawa da shi da kan shi zai zo ya tafi da ita. Ticket din nata ma one way ya siya mata.

Kallon lallen da Hafsatu take zana mata tayi tare da ajiyar zuciya ta ce. "Hmmm Maman Walid nima ban sani ba. Sai dai abun da Allah yayi kawai"

Tana ji a cikin ranta in har ta tafi to dawowar ta zaiyi wuya.

Shi gogan ma shirin maida makarantar tata can America gaba daya yake. Shi murna yake yi ma saboda an shiga yajin aikin. Don kwata-kwata basu saka ran sake haduwa ba sai nan da wasu 'yan watanni idan ta samu hutu. Sai gashi kuma Allah ya juya lamarin.

Maman Walid ta jinjina kai.
"Allah sarki Adda. Auren kenan fa. Tun da kike nasan baki taba tunanin ko da barin garin nan ba, sai gashi kasar ma gaba daya zaki bari.To dai in an tafi kar a manta da mu. A rike zumunci dan Allah. Nasan da wuya, amma ayi kokari Adda kinji?"

Nan da nan hawaye suka taru a kurmin idon ta. Ita ta isa ta manta da Maman Walid bayan irin kalar halaccin da ta musu. Ai ba ta isa ba.

Hafsatu ta dago ta kalleta tana dariya tace "Maman Walid kiyi shiru fa kar ta fashe mana da kuka a nan yanzu muji saukar jirage ta ko ina"

Dariya suka saka su biyun in da ita kuma Fareeha ke hararar Hafsatun.

Haka suka gama lallen suna dan taba hirarsu.

Sai bayan la'asar tukunna Hafsatu ta tafi bayan ta wanke mata lallen. Tubarkallah Masha Allah yayi kyau matuka. Ga fatar ta nan sai sheki takeyi da sulbi don kafin ta taho Azare sai da Anti Bebi ta kaita a ka mata gyaran jiki na tsawon sati biyu.

Ita kanta sai da taji canji a tattare da ita.

Tana share tsakar gidan bayan tafiyar Maman Walid ne Abba yayi sallama ya shigo.

Ledar Viva dake hannunsa ta yi sauri taje ta karba.

"Kaji ne nace ko zaki masa dambu ki tafi masa da shi?"

Sunkuyar da kai tayi tana murmushi. Allah sarki Abban ta. Dukda larurar dayake fama da ita, amma hakan bai sa ya dena musu dawainiya ba.

"Abba angode Allah ya saka da alkhairi ya kara budi."

Ya amsa da "Ameeen" kafin ya shige falon sa.

Tana cikin tafasa kajin Umma da Anti Mami suka dawo. Sun je dubo Daada ne a Shira ta danyi ciwo na kwana biyu har aka kwantar da ita a asibiti amma jikin da sauki yanzu Alhamdulillah. Fareehan ma ta so ta bi su amma Umma ta hana wai salon yawo ne kawai tun da dai mijin ta gida yace tazo bai ce ta je har wani garin ba kuma.

Leda cike da kwalam suka kawo mata wai inji Daadar. Haka tayi ta budewa tana ta murna. Su yajin tafarnuwa ne da daddawar miya da busashiyar kubewa da dai sauran abubuwan mutanenmu na kauye. Sai kuma chin-chin, gyada amaro da aya mai siga.

"Ke yanzu aka bude akwatin ki aka ga daddawar miya ai hana ki tafiya za'a yi" Anti Mami ta fada tana mata dariya.

Fareeha tayi narai-narai da ido. "Adda Samha fa tace baza'a kwace ba in dai nayi wrapping dinsu da kyau"

MaktoubKde žijí příběhy. Začni objevovat