28.

740 117 105
                                    

Barkanmu da Sallah jama'a ta🤍. Allah ya karba mana ibadunmu yasa munyi karbabbe ameen ya mujeeb.
Here is the long awaited chapter. Even though it's half baked, I couldn't resist giving you guys a goron sallah.
Allah ya bar min ku ❤.


28.

MANHATTAN, NEW YORK

"Wai lafiyar ka kuwa?" Mujahid ya tambayeshi a lokacin da suke fitowa daga masallacin Masjid Manhattan inda suka gabatar da sallar Juma'ah.

Mu'azzam ya danyi murmushi yana sosa sajensa.

"Me ka gani?"

Mujahid ya daga girarsa guda daya "Ga abun da nake gani kuwa. Tun dazu sai murmushi kakeyi kai kadai kamar sabon kamu"

Murmushin Mu'azzam ya fadada "Sabon kamun ne ai" ya bashi amsa yana sanya hannayensa a aljihun jacket dinsa. Yanayin bazara wanda turawa ke kira da Fall shine ke karatowa don haka wasu lokutan akan yi iska mai sanyi da ratsa jiki shiyasa yanzu ya zama ma'abocin sanya jacket.

Mujahid ya girgiza kai jin amsar abokin nasa "Something smells very fishy. Tunda ka dawo na ga ka fara wani walwali kaman sabon ango. Ko dai ko dai?"

Yau sati daya kenan daya dawo daga Najeriya.

Idan aka ce a kwana bakwai dinnan a kan gajimare yake yawo bazai musa ba don gaba daya wani sakayau yake jin sa.

Abun kam yanzu ya dena bashi mamaki. Ya dade da karban lamarin Fareeha a matsayin alkhairi a rayuwarsa, amma bai kara kaimin rikon da yayi mata a zuciyar sa ba sai da ta furta masa da bakinta cewa ta amince da kudurinsa a kanta.

Ba kalmar so ta furta masa ba ko wani muhimmin abu, amma a lokacin ji yayi kaf duniya babu mai sa'a irinsa.

Ji yayi komai ya daidaita a rayuwarsa, don ya gama hango yadda zai cigaba da tsarata tare da Fareeha a cikinta. Babu tantama kuma yasan zatayi albarka.

Lallai abun da aka gina shi akan turbar Allah shi ne yake wanzar da natsuwa da kwanciyar hankali a koda yaushe.

A duk lokacin da yake makale da waya ya ke mata hira, sai yaji kaman an sake wani sabon Mu'azzam. Shi kanshi bai san cewa zuciyar shi zata taba son wata bayan Najmarsa ba, amma sai gashi kullum kara dilmiya yake akan Fareeha. Dariyarta, murmushin ta, kunyarta kai har ma da tsiwarta duk burgeshi suke. Musamman ma tsiwar ta. Wasu lokutan da gangan kawai zai kunno ta don kawai ta mishi wannan tsiwar, hakan na sashi nishadi matuka.

Ranan ta ga gano shi kuwa turbune fuska tayi kaman yana kallonta tace "Nifa gaskiya da ba haka nake ba Uncle Captain, kai ne ke sakani yawan masifa"

Dariya yayi a lokacin shima yace "Nima da can ba haka nakeba Fareeha, son ki ne ya maida ni haka"

Dif tayi kamar bata wuri.

Lokuta irin haka idan ya ji tayi irin wannan shirun dadi yakeji don yasan cewa kalaman shi suna tasiri a kanta. Nan bada jimawa ba kuma ita ma zata fara mayar masa da martani.

And he couldn't wait.

Tasbihi yayi wa ubangiji yayin da suka karasa takawa wajen motar Mujahid inda ya faka ta. Mahaifiyar Mujahid din ta gayyace su cin abincin rana a gidan ta don haka tare zasu wuce.

A hanyarsu ta tafiya abokin nasa yana ta bugun cikinsa don yaji mai ke faruwa da shi amma sam ya ki fada masa. Ya fi so sai magana tayi karfi tukunna ya sanar dashi. Kuma yana da yakinin cewa nan ba dadewa ba zatayi karfin. Burinsa kawai a mallaka masa Fareeha a matsayin matar sa. Don haka tana gama jarabawa zai tura kanin mahaifinsa yaje wajen Baba Zubairu; gemu yaga gemu.

MaktoubDonde viven las historias. Descúbrelo ahora