18.

694 119 153
                                    

Your comments and unwavering support on the previous chapter  drove me into writing this one. You guys are the absolute besssttttt💗❤. Allah ya bar mun ku Ameeen.






"Kun shirya?"

Bata dago ta kalleshi ba ma tana sake cusa pencil case dinta a cikin school bag dinta tace "Eh".

"Ina Yusrahn?"

Ita tunda aka ce shi zai maida su makaranta taji gaba daya ranta ya baci.

Bayan sun gama yanke shawara ita da zuciyarta akan ya kamata a tattara Ya Ashraf da komatsansa a aika su waje, amma ta yaudare ta ta je ta boye shi a wani lungun zuciyar wanda bata san da shi ba. Sai bayan an gama biki da suka dawo gidan Bappah ta ganshi sai taji son shi ya dawo mata sabo fil. Abun da ya kara sata taji ta tsani kanta saboda wannan wani irin masifa ne?

A da ta yi tunanin watarana hankalinsa zai karkato zuwa gare ta shiyasa ta bata lokaci tana ta renon sonshi amma yanzu da ta fahimci bata ma gabansa ba sai ta hakura ba? Sam zuciyarta taki yarda da hakan. Sai ma wasiwasi da take saka mata.

To wa ya ce miki ita din sonta yake? Kin ma san wacece ita? Don ya saka ta a wallpaper ba lallai son ta yake ba. Watakil ma ta mutu kawai yana so yana tunawa da ita ne. Wa iyazubillah.

Daga karshe kawai ta yanke shawarar rage haduwarsu a gidan. Tana tashi da sassafe zata fito tayi abubuwan da zatayi sai ta koma daki, har sai taji karar fitar motarshi a gidan sannan zata fito parlor. Duk inda karfe biyar kuma tayi zata sake komawa daki ta buya don tasan ya kusa dawowa gida.

Wasu lokutan idan ta manta bata shiga da wuri ba to tana jin muryarsa zata sulale ta gudu daki.  Kuma sai taci sa'a in de ta shigo daki ta buya kuma babu me nemanta balle ma ta fito ta ganshi. Hakan ya fi mata, don ya rage mata radadin da take ji a zuciyarta. Wasu lokutan ma in ta kwana biyu bata ganshi ba har ta na mantawa da sha'aninsa. Sai anyi rashin sa'a wani ya ambace shi ko kuma taga giftawarsa sai abun ya dawo mata sabo. Wannan wace irin masifa ce?

Gashi yanzu ya fito ya tsaya a kanta yana ta mata wasu tambayoyi, yana kara karya mata zuciya.

"Tana fitowa" ta amsa mishi tare da saba jakarta ta shige kitchen. Ba komai za tai a kitchen din ba kawai ganin sa ne bata son yi don a yanzu kam ji take kaman ta amayar masa da abunda ke cikin ranta ko zai fahimci irin rudanin da ta ke ciki. A yadda take jin tan nan da zai ce yana son ta koda na minti biyu ne to komai zai daidaitu a rayuwarta.

Nan da nan kuma ta kara jin haushin kanta. Shin Fareeha ke mayya ce?

Wasu hawaye ne masu dumi taji suna gangarowa kan kuncinta. Tun da abunnan ya faru take so tayi kuka ta kasa amma sai yau? Nan ta kife kanta a kan worktop din kitchen din ta kara fashewa da wani kukan.

Amina ce ta shigo ta kofar baya da shanya a hannunta ta same ta a wannan yanayin. Ta yi saurin isa gareta tana dafa ta. "Adda Fareeha meya sameki?"

Kokarin hadiye kukan take amma ta kasa. Kai kawai ta girgiza mata.

"Ko komawa makarantar ne bakya so?"

Ta sake girgiza mata kai hade da dagowa daga kifuwan da ta yi. Ta sa gefen hijabin ta tana share hawayen ta. "Nima ban san meyasa nake kuka ba fa" ta fada tana yin tsaki. Kwana biyun nan kam ta koyi tsaki abun har mamaki yake bata. Kuma duk lefinshi ne.

Ta karasa bakin sink ta bude ta wanke fuskarta.

"To kiyi hakuri. Ai komai ya zo karshe inshaAllah"

Murmushi tayi wa Aminan. "InshaAllah"

MaktoubWhere stories live. Discover now