13.

700 107 51
                                    

Hazo ake na ban mamaki a garin dayake sanyi ya shigo gadan-gadan. Rigar sanyi ce a jikinta wacce takai har wuya (turtle neck) kalar sararin samaniya. Ta dora doguwar rigar atamfa mai guntun hannu don haka dogon hannun rigar sanyin ya fito. Kanta sanye yake da hular sanyi fara sai dankunneta fari na beads shima dayake ta lilo a kunnen nata.

Kunun gyada take hadawa. Jiya da suka dawo a makaranta da rana taji Anti Bebi tana zancen za'ayi kunun gyada da safe kuma sai taji kwadayin kunun ya kamata ita ma. Don haka tunda tayi sallar asuba sai tayi wanka ta fito. Ta samu Amina tana sharar falo ta tambayeta ko Mama ta mata zancen kunun tace a'a. Kitchen din ta wuce kai tsaye.

Bata san inda gyadar take ba amma a bincike binciken ta ta samo ta markadaddiya a store. Babu bata lokaci ta hau aiki.

A lokacin Anti Bebi ta shigo kitchen din. Har a lokacin idonta cike yake da bacci. Ko wanka batayi ba don rigar bacci ce a jikinta sai hijabin da ta dora akai.

"Ayyah Fareeha am. Da sanyin safiyan nan? Ke kam bakya gajiya ko?"

Tayi murmushi "Mama ina kwana?"

"Lafiya Alhamdulillah. Ke da kika dawo hutu zaki hau wani aiki? To meyasa baki taso Yusrah tazo ta tayaki ba?"

A jiyan aka basu hutun karshen shekara wanda ya kan kama daga tsakiyar December zuwa farkon January. Bappah ne ya zo daukansu shi da Ya Ashraf wanda hakan ya zame musu surprise don basu tsammaci ganinsa ba. Shima hutun yazo. Kwanansa biyu da zuwa kuma daya samu labarin za'a zo daukarsu yace ze biyo Bappan.

Yusrah kam tasha murna sosai dan bata shiri da kowa kamar yanda suke shiri dashi kuma tayi kewarsa sosai. Haka tayi ta mishi surutu a mota har sukazo gida. Ita kam Fareeha tun bayan gaisuwar da sukayi bata kara cewa uffan ba.

Har bayan sun dawo gida ma Yusrah bata barshi ya sararara ba. Duk inda yayi tana biye da shi. Har dare suka kai suna hirar yaushe gamo. Don Fareeha bata ma san yaushe ta shigo daki ta kwanta ba. Shiyasa ma yanzun bata tasheta ba don tasan bacci bai isheta ba sosai.

Ta dan rausayar da kanta tana murmushi tare da jujjuya gyadar da hannunta a cikin robar da ta saka wa ruwa "Mama bakomai wallahi. Ai aikin babu yawa"

Anti Bebi ta jinjina kai kana ta wuce wajen fridge inda ta saka naman kan data dafa jiya da daddare ta ciro shi.

Tukunya ta samu ta juye shi a ciki sannan ta dan kara ruwa akan ruwan romon dake jikinsa wanda yasha citta da daddawa kafin ta shiga saka mishi spices da markadadden kayan miyan da bata rabuwa da shi a freezer dinta koda yaushe. Farfesun naman kan takeson yi don aci da masa wanda tayi order tun jiya da yamma.

Tare suka cigaba da aiki suna dan hirarrakinsu. Yawanci Maman ce ma take tambayarta akan makarantar tasu ita kuma ta bata amsa.

Da sallama ya shigo kitchen din ta kofar baya. A tare suka amsa masa sannan Fareeha ta gaishe shi. Ya amsa hade da jawo wata kujerar tsuguno ya zauna akai.

Tunda ya shigo ta ji ta nemi nutsuwarta ta rasa. Ko a jiya ma da suka gaisa a harabar makaranta sai taji zuciyarta ta buga. Ta zaci ko zumudin zuwa gida ne ko kuma wani abu. Amma yanzu da hakan ya sake faruwa sai ta yadda lallai saboda shi ne.

To meyasa? Tsoronsa take ko me? To rabonta da shi tun yaushe har za ta fara tsoronshi? Dama can ba wani saninsa sosai tayi ba.

Da wannan sakar zuci ta juye gyadar a cikin tukunya sannnan ta daura ta akan wuta.

Hirarsu suke shi da mamansa, ita kuma ta kasa sukuni Allah Allah take ta gama aikinta ta bar kitchen din.

Suna haka sai ga Fadila ta shigo kitchen din itama. Waje ta samu ta zauna kusa da Ya Ashraf tana ta mutsutsuka ido.

MaktoubWhere stories live. Discover now