1.

11K 543 132
                                    

Brooklyn, New York.

Litinin, 12th June 2012.

Hawaye ne masu bala'in zaafi suke zubowa daga idon Ibrahim Mu'azzam a lokacinda mahaifiyarshi dake gefenshi take qoqarin kwantar mishi da hankali. Sai dai kash! Itama kukan take don haka sai ta kasa lallashinsa domin itama a lokacin tana buqatar lallashi da ban baki. Zaune suke a waiting room din A&E unit din Parkway Hospital. Mintina talatin da suka wuce kenan aka sanar musu rasuwar matar Mu'azzam wato Najma wacce ta shaafe kusan kwanaki biyar tana fama da jinyar ciwon bronchitis.

Kuka sosai Mu'azzam din yake har da shesheqa. Wata nos ta qaraso wajensu fuskarta babu yabo babu fallasa ta ce "Mr. Kabir, you may go in and take the body".

Jikinsa na rawa haka ya miqe ya bita zuwa dakin daukan gawa.

Gawawwaki ne gasu nan an jerasu a sahu kowa da sunansa da lokacin mutuwarsa a lankaye a jikin gadonsa. Dukkan gawawwakin na jiran family member yazo ya tafi dasu kamar yadda tsarin asibitin yake. Ya tsaya a kan gawar Najmar wanda tuni an rufeta a cikin wani silver yadi.

Name: Habib Najma

Age: 21

Time of death: 11:54am.

Abunda aka rubuta kenan a jikin gawar tata. Wasu hawayen suka sake kwaranyo masa. Ya kira sunan Allah tareda jan dogon numfashi kafin nan ya turata izuwa waje.

Ammah dake durqushe ta miqe ta nufo shi. Babu abunda bakinta yake furtawa sai 'Innalillahi wa inna ilaihi raaji'un'. Ta sa hannu suka tura gawar tare zuwa waje inda motar daukan gaawa take. Basu zarce ko ina ba sai community masjid din da ke unguwarsu.

Da qarfe biyu bayan sallar Azahar aka sallaci Najma Habeeb kuma aka miqata izuwa ga makwancinta wato qabari. Mutane da dama wadanda ta qulla alaaqa da su a 'yan shekarun da tayi a garin sun hallacci jana'izar tata.

Babu abunda suke fada a kanta sai alkhairi domin Najma ta kasance mai faran-faran da mutane ga son taimako da girmama na gaba.

Kawayenta da sukai internship a United Nations headquarters tare sun zubda hawaye kuma sunyi kewarta matuqa domin ta riqe su kamar 'yan uwanta na jini.

Amma duk cikin ilaahirin mutanen nan babu wanda yaji mutuwar ta har cikin bargon qashinsa kamar mijinta kuma masoyinta wato Mu'azzam. Ji yake kamar an sa wuqa an yanke wani sashe na haqarqarinsa ne.

A lokacin ne wani zazzafan zazzabi ya rufe shi. Ya dawo da qyar ma yake numfashi. Hankalin Ammansa ya tashi. Kafin Maghreba tuni an kaishi asibiti. Ai babu shiri likitoci sukayi admitting dinsa. Ammah ta rasa mai ke mata dadi. Da rashin Najma zataji ko kuwa da Mu'azzam danta tilo guda?. Haka tai ta kaiwa da komowa a asibitin har sai da ta tabbata ya zama stable sannan hankalinta ya dan kwanta. Ta zaro wayarta domin sanarda mahaifan Najma rasuwarta amman sai ta rasa da irin muryar dazata fada musu. Ta yanke shawarar kawai tayi musu text message. Hakan kuwa akayi.

Bayan likitoci sun gama zurkuda masa allurai kuma an saka masa drip, wani nauyayyan bacci yayi awon gaba dashi. Ammah na gefensa tana karanta masa Suratul Baqara murya qasa-qasa. Bada jimawa ba itama baccin yayi awon gaba da ita domin stress yayi mata katutu a system dinta.

Ba ita ta farka ba sai qarfe daya na dare. Bandaki taje ta dauro alwala tazo ta gabatarda sallar Isha'i domin bacci bai barta tayi sallar ba akan lokaci ba. Tana idarwa ta dago wayarta dake kan kujerar datayi bacci akai.

Missed calls ne kaca-kace akai. 'Yan uwan Najma da mahaifanta sun mata missed calls kusan ashirin. Da suka ga sun kasa samunta sai suka mata message cewar zasu zo har New York din nan ba da dadewa domin suzo suyi wa Mu'azzam din ta'azziyah.

MaktoubWhere stories live. Discover now