11_12

739 59 6
                                    


🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

SADAUKARWA GA ƘUNGIYAR PERFECT WRITERS ASSOCIATION, DOMIN TAYA MURNAR CIKA SHEKARU BIYU DA KAFUWA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.

Afuwan banyi Editing ba





11_12


Amsa mata Sallamar sukayi, ta shigo ɗauke da jakarta ta matafiya, Imran na jin muryarta ya miƙe ze fito, Alhaji Hashim ya riƙe shi yace
"Imran, kabi komai a hankali"

Imran ya jinjina kai ya fito, Abba cewa Yake "Imran yi a hankali, banda fushi nan naka"

Imran Yana fitowa sukayi ido huɗu da Amira, seda cikinta ya juya amma tai banza kamar bata ganshi ba, tana ƙoƙarin shiga ɗakinsu.

"Ke daga ina kike?!"

Yai mata wata razananiyar tsawa, seda ƙirjinta ya buga da ƙarfin gaske, amma tai banza da shi, ta fasa shiga ɗakin ta ajiye jakarta a tsakar gida, ta samu guri ta zauna tana tauna cingam ɗin bakinta, tana jiran Imran yai mata duk abinda yaga dama.

Alhaji Hashim ne suka fito tare da Abba, Amira ta ɗaga kai ta kallesu, sedai kallo ɗaya tai musu ta ɗauke kanta, saboda yadda take jin haushin Abba daga shi har iyalansa, haushinsu take ji.

Alhaji Hashim yayiwa Imran alama da ido sannan ya kalli Amira yace "Masha Allah, ashe wannan ce 'yar tawa da kake bani labari, tubarkallah gata me kyau kamarka ɗaya da ita, a bamu tabarma mu zauna daga nan mu gaisa da ita"

Yai maganar yana nazarin Amira, kasancewar sa masani a fannin kimiyar sanin halayen ɗan Adam.

Kana ganin shigar jikinta zakaga fitinaniya, bata kuma kallonsu ba ta ɗauke kanta tana wasa da yatsun hannunta, Imran kam kamar ya ɓarar da ita haka yake ji.

Aka miƙo tabarma Abba ya shimfiɗa suka zauna, ita kuma Amira na kan turmi, ganin sun zauna ita kuma tana sama, yasa ta miƙe zata bar gurin.

Alhaji Hashim yace "ina kuma zakije?"

"Ɗakinmu mana" ta bashi amsa kai tsaye, shi dai Abba yakasa cewa komai se binsu da ido.

Alhaji Hashim yace "haba Amira muda muka zo ganinki se kuma ki tafi ki barmu?"

Amira tace "Niba gurina kuka zo ba, kunzo gurin mutanen gidan nan ne, dan a gaya muku halina kuma an zauna an gaya muku komai, kuma in zuwane ai a baya Yakamata azo a ganni ba a yanzu ba"

Tai maganar ƙwalla na taruwa a idonta.

A hasale Imran yace 'Ke ana miki magana zaki yiwa mutane rashin Kunya?"

"Karka ƙara yimin tsawa na gaya maka, akan me ina ruwanka dani? Tunda kazo ban kulaka ba meye nayimin tsawa" Amira tai maganar cikin tsiwa.

Imran ya harzuƙa, amma Alhaji Hashim ya girgiza masa kai yace "Yaya Imran gaskiya ka dena yi mata tsawa, kai baka san lallaɓa ƙanne akeyi ba, ai nan ba barikin soja bane, zoki zauna mu gaisa mana"

WUTA A MASAƘAWhere stories live. Discover now