7

955 37 6
                                    

*♡SIRRIN ƊAUKAKA♡*
_Wattpad@ayshajb_

®️🌁

*FARIN JINI WRITER'S ASSOCIATION..📚📚*
[Kungiya Domin wayar da kan mata, Farin jini writer's domin ci gaban Mata.]

_♡F.J.W.A♡_

https://www.facebook.com/FARIN-JINI-Writers-Association-109861227874440/
Jama'a ga sauki na buga kofar gidanki batareda kin sha xafin rana ba,ko kinsan SHANONO AND SODA CLOTHES AND MORE Suna bajakolin kayan Atamfofi kayan kicin tsantsara tsantsara na kece raini? To banan suka tsaya ba akwai abubuwan da suke order bayan wannan cikin aminci da kwanciyar hankali a rabu ana madalla.
Kishiga wannan group domin kashe kwarkwatar idonki.
Sannan Ga nambar daxaki iya kira ko chat da ita domin neman karin bayani
👉👉👉 08137145294
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/FQ9k6e5aOljEP3s3UGqEcu
Telegram group
https://t.me/joinchat/V8pGp9ceSc4zYWNk
7..
Tunda nayi sallar subayi na koma azkhar dinma da kyar nayi domin wani i'rin mugum kasala nake ji, kwanciya nayi Hanisa da Halima sun fita domin al'adace da zaran mun idar da sallah zamu fita munyi shara mu gyara gidan duk da akwai masuyi Ummi bata sangartamu ba, aiki muke sosai domin nike girki Sabida bala'in kaunar abinci na mayar da hankali sosai gurin karance karance littafan girki ban b'ata lokaci gurin karatun novels, kamar yanda na maida hankalina gurin, Girki Hanisa kuwa gwanace gurin had'a turaruka masu kyau da khamshi Tawa Halimat an barta gurin zanen lalle da kitso,

"Masha Allah yan Mata na sannunku ubangiji ya baku mazajen Auren nagartattu Wanda zasu rike mu ku, rabbi ya maku mazan da zasu d'aukaka daraja da martaban ku, inna Hauwa?" Ta karashe maganar tana tambayar su, murmushi sukayi dukk'an su, cikin jin dad'in addu'ar ummi Hanisa tace "Ameen Ummin mu, Jiddah bata jin dad'i tana kwance d'aki" Halima ta karb'i zancen da fad'in "ummi bansan abinda ke damunta ba, ko magana bata son yi"

"Subhanalillahi bari na dubata"

Hanyar d'akinsu tayi,

"Wallahi duk se naji wani iri in-law, ba lafiya" cewar Hanisa kamar zata fashe da kuka Haka tayi maganar..

Ajiye wukar da take yanka lawashin albasa Halima tayi "bari kawai nima karfin Hali nakeyi Amma na damu da sahiba sosai" cikin mutuwar jiki suke aikin tare da jin ba dad'i rashin kasancewarta tare dasu ..

Damuwar da take ciki be hanata yin Sallama ba domin haka kawai take jin kaunar yarinyar sosai inna kwance zazzab'i nake ji a hankali na amsar Mata sallamar zama tayi a gadon tare da kama hannuna "ummi.." na Kira sunanta tare da fisar da iska , wani zafi ne, yake fita a bakina. "Sannu Hauwa Allah ya kara miki lafiya shine bazaki sanar min ba? Me yasa kike barin damuwa a ranki ni amatsayin 'Ya na d'aukeki keda Halima baku da banbanci gurina Amma naga yanda na d'aukeki ba haka kika d'auke ni ba."

"Ummi.." kukan da take dannewa tun d'azun ne ya kwace mata a hankali na matso jikinta tare da kwantar da kaina saman kafad'arta wani i'rin kuka nake Wanda banson ma'anarsa ba, nasan inna kewar iyayena sosai inna cikin maraici da kad'aici "waya tab'amin shaleleNah? (A duk lokacin da take son rarrashi na wannan sunnan take kirana dashi), Hanisa ce ko Halima? Fad'amin kinji Shalele.." wani i'rin murmushi nayi tare da sauk'an hawaye runtsa ido tayi domin duk na b'ata Mata jikin Himar d'inta (Wai dan Allah ke yar Borno ce yawanci haka kike ambatar Sunan Hijjab wanda suma yan Borno Haka suke Kira jama'a na yawan min wannan tambayar,)

"Ummina basu bane bansu bane! 'Yan uwana basu min komai ba, hasalima sun damu da damuwata ummi zuciyata zafi take min, bugawa takeyi banajin dad'in komai bana ganin komai da haske ya zanyi ne Ummi?" Na fad'i Haka inna kara fashewa da sabon kuka, "kiyi hakuri ki ringa addu'a ki dena biyewa shed'an da rud'in zuciya ki ringa nutsuwa kina ibadarki kinji sannan ki yawaita sadaka domin babban maganice kina da ilimi kina da sani Amma meyasa kike barin shed'an la'ananne yake galaba akan ki? Haba Shalele" ajiyan zuciya na shiga saukewa sakamakon shafa kaina da take rik'e d'ayar hannunta nayi sosai "insha Allahu Ummi zan ringa kokari"
"Yauwa Yar albarka bari na Kira likita ya dubaminke.." da sauri nace.
"A'a nasha magani ummi zanji sauki"
Batason jayayya dole yasa ta kyale ni tea ta had'amin da kyar nasha ta Kuma bani magani Daman bansha ba kawai bana so ta Kira likita ne.

Kamar kwai haka take lallab'ani wunin ranar ta bani kulawa domin ko makaranta bata je ba, ganin haka yasa suma sukace bazasu jeba, seda ta tsawatar musu suka tafi kwana biyar inna kwance Alhamdulillah nayi dama domin inna tayasu da wani aikin, kasancewar lahadi ne yasa da yamma Ummi tace in shirya zamuje sayayya haka muka shirya dukkansu Suna zumud'i Banda ni da nake jin zuciyata babu dad'i, i'ta take Jan motar har muka iso wani babban shago duk muka fito mun faka motar mu gaban wani had'add'en bakar Jeep shiga mukayi a hankali muka fara shagayewa kowa na daukar abinda yake so Banda ni, da duk nake jin wani i'rin sanyi na shiga jikina gaba nayi da kwanton hannuna na fara d'iban kananun kaya brezia pants da riga shimi da shomshort haka kawai na tsinci kaina da d'ibansu duk da ni ba ma'abociyar saka su bane, musamman ma bran, domin nonuwana Tasa ne (irin nonuwan da suke Nan cur d'as suke Zaune a qirji daga kasa akwai fad'i sun baje Amma nipples d'insu a cure yake a tsakiya nonuwa Wanda ko yara goma aka shayar sunanan da k'yansu basa zubewa) murmushi kawai nake zabgawa wanda rabon da inyi har na manta, shigowarshi kenan ta tasa shi gaba tana mishi surutu shi kuwa bema san tana yi ba, kaya yake d'iba mata wayarta da aka kirane yasa ta yin shuru tare da matsawa gefe tana amsa wayar na gama d'iban kayana juyawar da zanyi cikin rashi sa'a na bangaje mutum tsantsine ya d'ib'eni duk kayana sun tsarwatse cikin zafin nama ya finciko hannunta tare da rumgumeta a faffad'an qirjinsa wani i'rin ajiyan zuciya suke sauke tare,
Kara matseta yayi sosai qirjinta na gugan nashi zuciyarta wani i'rin bugawa yake Wanda yasa yake jin nonuwanta sosai a jikinshi wani i'rin juyi yayi da hannuwanshi a kuqunta , yarrr tsigan jikinta ya tashi a hankali ta bud'e idanuwanta masu kama dana mage gata da mik'akk'un gashin ido masu tsawo kurawa juna ido sukayi wani i'rin kallo yake mata wani i'rin matsiyacin gudu matashiyar budurwan tayi har tana wani sufa tsaban kishi wata take kallo jikin abin sonta Wanda ko da wasa be tab'a kwatanta mata kallon da yake mata ba, inba gizo idonta ke Mata ba, kad'an ya rage bakunansu be had'u Dana juna ba.

Jin ihuta ya ankarar dani da sauri na kwanci kaina cikin rashin kuzari nace "kayi hakuri dan Allah ban lura da Kai bane" shuru yayi bece min komai ba kayana na kwashe "dakata zan Miki kashedi Nabil nawa ne ni kad'ai dan ni Akayi shi shegiya me idon kuliya, kin wani manne mishi kina mishi kallon karuwai to Mijina yafi karfin ki.." murmushi kawai nayi domin sarai kishi ke d'awainiya da i'ta Amma kalamanta sunfi zafi tafiyata nayi Nan ta shiga mishi masifa kala yanda kuka San dutse haka ya mayar da i'ta siyayyar da basuyi ba kenan ,

Na samesu tsaye ni suke jira a hankali na Mika kayana aka saka min a leda Ummi ta biya muka nufi mota waigawar da zeyi ya yanga tana kokarin shiga mota kamar wacce akace in juya ai kuwa mukayi ido hud'u wani i'rin had'add'en murmushi ya sakar min Sunkuyar da Kai nayi tare da shigewa motan, Nan Halimatu ta hau mita "haba sahiba duk kin shanyamu wai inna kika tsaya naga ba kayan arziki kika d'iba ba?" Murmushi kawai nayi "ban son isk'anci ya inna Miki magana kin min banza!"

"Toh uwar masarasa hakuri kin cika Mana kunni " cewar Hanisa cikin zolaya tayi maganar harara ta mata sanin bazatayi magana bane yasa nace. "in-law bana so fa babu wandan ya kai sadiyata hakuri bana so fa!" Cikin marerecewa nayi maganar inna kallon Halima tare da bata hakuri da ido juyar da kanta tayi jikin glass tana kallon titi hannunta na rike domin sarai fushi take dani "Ummi ki taya ni bada hakuri dan Allah Hali dubu tayi fushi" _banzaye kawai_ cewar Hanisa cikin zuciyarta. "Yi hakuri to Halimatutu" dole yasa ta murmusa domin cikin zolaya ummi tayi maganar.

Haka muka karaso gida muka baje a falo Yahgana ta kawo Mana abinci tare da Mana sanda zuwa kowa ya bud'e kayanshi Amma ni na kasa domin Wallahi kunyar Ummi nake ji, "muga kayanki Jiddah cewar Hanisa" zubur na mike na shige d'aki batare da na d'auki kayan ba kai hannu tayi zata bud'e kayan Halima tace. "Kinga karki bud'e mata kaya" harara ta watsa mata tare da jawo ledar tana shirin bud'ewa Ummi tayi murmushi. "Barshi Hanisa" badon ranta yaso ba tabar kayan, "Kuje kuyi haraman sallah domin magrib ta gabato."

D'aki sukayo lokacin na fito daga band'aki bayan nayi alwala sallaya na shimfid'a "ki gama wallahi sekin bud'e na gani" murmushi na sakar mata, Halima tace "dake mayyace Wallahi zaki cinye mutum har kashi! Nacin ki yafi na kowa"

"Oho de sena gani"

*Maman Faruq*

SIRRIN ƊAUKAKAWhere stories live. Discover now