11

50 3 0
                                    

*KWANTAN ƁAUNA*
         FitattuBiyar 2023

             ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*011.*

       Maimakon ya wuce gida samun kansa yayi da nufar gusset house d'in mai martaba da yake hannun sa ya shiga ya faka motar ya shiga cikin gidan, a kan kujera ya zauna yana sauke numfashi a wannan lokacin kiran Zaid ya shigo wayar sa, d'auka yayi dan yasan maganar guda d'aya ce ya ya sauka kuma daman abinda ya tambaya d'in kenan. Ajjiye wayar yayi yana kallon wani waje daban kafin ya kulle idanun sa hoton ta yana gifta masa a idanun sa.

         Tuno fuskar da aka zana masa yayi ya tuno fuskar yarinyar da ya taimakawa a bayyane yace, "Akwai kama sosai, kenan suna da relation?." Sai kuma ya dafe kansa a zuciyar sa yace, _Why Asad meyasa wannan zai dame ka?, kawai dream ne fa ba gaskiya bane, ka manta da wannan tunanin ko zaka samu peace of mind._ numfashi ya sake saukewa a bayyane yace, "but why nake ganin ta a mafarki always tana taimako na?."

        Sai kuma ya mik'e tsaye yana fad'in, "ya kamata na nemo wannan yarinyar" Sai kuma yaja ya tsaya ya kama k'ugu ya fad'a kan kujera ya zauna yana furta, "Oh Asad!" Ya dafe kansa yayi shiru yana sauke numfashi a hankali tunanin yake barin ransa ya runtse idanun sa yana goge fuskar ta mafarki da wacce aka zana masa a hankali suke barin idanun sa yana ajiyar zuciya.
Ya jima a haka sosai har magariba tayi a nan yayi sallah kafin ya mik'e ya d'auki key da wayar ya fita ya shiga mota ya fita daga gidan.

          Baiyi gida ba babban company sa ya wuce ya tarar da Hafiz yana ta kai kawo har lokacin ganin sa ya shigo ya saka shi bin bayan sa zuwa office suna zama Hafiz yake cewa, "Asad what happened?." Bai bashi amsa ba yayi shiru ya jawo laptop d'in dake kan table d'in gaban sa yana dannawa. Ganin hakan sai Hafiz ya bar shi ya fita bai jima sosai ba ya fita daga office d'in yaja motar ya fita gabad'aya.

          Gida ya wuce kai tsaye wajan Mama ya shiga kasancewar magariba ce bai same ta ba Suhaima take sanar dashi tana d'aki ya shiga wajan Hydar yana nan kamar yadda yake koda yaushe ko hannun sa baya motsawa yayi masa addu'a ya zauna a kan kujera yana kallon sa. A nan ya kwashe lokaci da yawa har i'sha tayi ya fita yayi sallah ya sake dawowa a nan ya ga Mama a wajan Hydar ya k'araso gaban ta ya tsuguna da girmamawa yace, "Barka da dare Mama."

"Ina kaje yau?" Ta tambaye shi ba tare da ta amsa ba. Kallon ta yayi sai kuma ya d'auke idanun sa wannan tun yana ganin wani abu kan tambayar nan da Mama take masa ta ina kaje, ina zaka, me zakayi in ka fita, wa ka tambaya har ya daina ma domin ya saba.

"Naje Abuja" ya bata amsa a tak'aice. Bata ce komai ba tayi jim kafin tace, "yaushe zaka je wajan Jidda kasan dai ita zaka aura ko?." Kallon Maman yayi baice komai ba tace, "in baka ce ba nasan ai ka jini, nan da lokaci kad'an za'a d'aura muku aure ta." Kai ya girgiza kafin yace, "Mamaa......" Sai kuma yayi shirun jin hakan sai tace, "kar kace min baka sonta ko baku dace ba, itace zab'ina ya zamar maka dole ka sota." Kai ya jinjina alamun gamsuwa kafin ya mik'e jikin sa a sab'ule ya fita.

      Sallama akayi aka shigo falon ana fad'in, "y'ar sarki, jikar sarki, matar sarki, babar sarki kuma k'anwar sarkin garin Kano in sha Allah." Jin muryar tasan wacece k'anwar mai martaba kenan Rabi'a kaf cikin dangin mai martaba tasu ce tazo d'aya suna shiri sosai ta juya ta kalle ta ta fad'ad'a murmushi tace, "babbar bak'uwa." Murmushi tayi mai sauti itama ta k'araso tana fad'in, "Zaman kujera ya gagare ni ni Rabi in dai har gimbiya na zaune a kai." Kan Mama ya sake fashewa izzar ta ta ninku ta saki murmushin k'asaita tace, "keda kika b'uya ko ganin ki ba'a yi."

"Yanzun ma dole ce ta saka na taso nazo domin naji abubuwa suna ta faruwa marasa dad'in ji." Mama ta sauke numfashi tace, "bari kawai Rabi'a komai yana neman lalace min lokacin da ban shirya ba."
"Shiyasa nazo ai naji ya akayi hakan take faruwa."
"Sharrin Hajiya ne, itace ta bama Asad guba a ganye yaci." Murmushi Tayi tace, "Zata aikata ai, in kince badaqalar da suke yi da waziri kare bazai ci ba. Waziri yayana ne amma bazan b'oye miki ba baya son ki baya son me son ki, kinga dashi da galadima dama kawai suke jira a kan ki su kawar da y'ay'an ki sabida a lalata maki goben ki."

KWANTAN ƁAUNAWhere stories live. Discover now