013

50 3 0
                                    

*KWANTAN ƁAUNA*
      FitattuBiyar 2023

             ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*013.*

Rai a b'ace Rauda ta shiga gida Khalil ya taimaka mata ta ajjiye sandar hannun ta ta zauna a kan farar kujerar da take tsakar gida shi kuma ya zauna a k'asa. Yanayin ta Umma ta kalla tasan an tab'o ta kuma tasan bazai wuce akan maganin ba hakan ya saka tace, "ko baki ce ba nasan ya hana ki maganin ne shiyasa kike kunbura fuska, sai kiyi hak'uri." Rauda tace, "daga neman taimako Umma sai ya zage ni? Har yana cewa da yasan halin Baba tun farko bazai bada bashi ba."

Umma ta murmusa tace, "ban ga laifin sa ba Rauda; yanzu kafin wannan kud'ad'e masu tarin yawa su fito daga hannun baban ki a shekara goma a fama. Yayi k'ok'ari fa da ya baki ma dan ba kowa ne zai bada magani mai tsada kamar naki ba, Allah yasa baki masa rashin kunya ba dan ya taimaka miki." Shiru tayi bata amsa ba Baba da yaji komai ya shigo yana fad'in,

        "In ma tayi masa rashin kunyar ita ta jiyo ai ita k'afar zata damu da ciwo sabida rashin magani bani ba." Shiru sukayi dukkan su kafin Khalil yace, "Umma wani kyakykyawa kamar balarabe ya kusa kad'e Anty yanzu har sai da ta fad'i k'asa." Umma tace, "Kuma dai?."
"Amma ai bata ji ciwo ba ai. Umma ta yi masa rashin kunya yace muzo ya kawo mu gida tak'i kuma baki ga motar ba babba" ya fad'a yana fad'ad'a hannayen sa alamun girma.

     Baba da yake alwala a durk'ushe furzar da ruwan bakin sa yace, "A koda yaushe ke ai bak'in halin ki yake ja miki alkhairi yake tsallake ki ya koma kan wanin ki. inda kin shiga motar da bai siya miki maganin ba." Umma tace, "Rauda akan me zaki masa rashin kunya? Meyasa ke baka jin kunyar yiwa babba rashin kunya ne?." Rauda tace, "Umma nifa ba rashin kunya nayi masa ba na fad'a masa abinda yake raina ne. shine wanda nace miki ya mare ni lokacin da na raka su Habiba gidan sarki shine na amayar masa da abinda yake zuciya ta a lokacin ban samu dama ba ina jin tsoron doki ya hana ni mayar masa."

Umma ta wara idanu tace, "D'an sarkin Katagum guda masu ji da kud'i da mulki kika yiwa rashin kunya Rauda?, Yaron da an masa shaida bashi da kirki ina ke ina shi?, in ya saka aka yi miki wani abun fa?." Rauda ta turo baki gaba tace, "To Umma dan yana d'an sarki sai yayi min abinda yaga dama na k'yale shi? Bafa haifata yayi ba da zai fad'a min magana na tsaya ina kallon sa, wallahi saina rama dan mutum ne shi nima mutum ce."

         "Sannu y'ar gidan dangote, nace sannu y'ar gidan shugaban masu kud'in duniya. Wato in ana neman talaka mai fad'in rai wanda aka fad'a a hadisi aka same ki Rauda an shafa Fatiha. Tunda bake ban tab'a ganin yarinya mai karanbani da nuna isa kamar y'ar wani ko y'ar wata sai ke da kanki yake rawa. D'an sarki guda kika yiwa rashin kunya, bakya jin tsoron wani abun ya same ki ke ga fitsararriya mai ji da fitsara. Har yace miki kizo ki shiga mota ya kawo ki kika ki sabida girman kai yayi miki yawa. To Allah ya isa abinda yayi niyar baki in ya kawo ki kika yi mana bak'in ciki da yau nasan kaji zamu ci mu kwanta, sakamakon rashin kunya duk abinda ya saka aka yi miki ke kika ja kar sunan Adamu ya fito a gaban sunan ki" Baba ya fad'a yana buge rigar sa ya fita.

      Umma ta girgiza kai tace, "Wai Allah ya isa, Malam har ya saka a ran sa ma za'a bashi wani abun bama illar shiga motar tasa yake hangowa ba kawai a bashi kud'i koma me yayi miki in kin shiga motar ke kika jiyo. Kai Allah ya kyauta" Umma ta fad'a tana murmushin takaici kafin ta kalli Rauda tace, "Kinga Rauda na raba ki da y'ay'an masu kud'in nan babu ruwan ki dasu in ba so kike ki jawo mana matsala muna zaune lafiya ba. Ina ke ina yi masa rashin kunya? In yaso a batar dake yana da damar yin hakan babu wanda yasan shine yayi, ki dawo hankalin ki dan Allah bana son wannan fitsarar taki." Rauda bata ce komai ba tayi shiru k'afar ta na ciwo rashin shan maganin da batayi ba.

*☆☆☆*

         Tun a mota yake tunani har ya isa guest house d'in mai martaba ya shiga kamar yadda ya saba shi kad'ai ya zauna a akan kujera yana sauke ajiyar zuciya. kallon katin yake yana kallon sunan ta kamar a jikin sunan yana so ya gano wani abun.  _Sa'ar ka guda nasan darajar d'an adam da babu abinda zai hana ban wanke maka taka fuskar da mari kamar yadda ka mari tawa._ kalaman ta suka fad'o masa a rai ya runtse ido jin abinda bai tab'a ji ba yana kawo barazana ga kunnen sa.

KWANTAN ƁAUNAWhere stories live. Discover now