ZAZZAFAR KAUNA 91-100

191 9 5
                                    

*🌺DA'IMAN ABADAN*🌺
        _ZAZZAFAR KAUNA_
*~HOT LOVE AND FATE STORY~*

*BOOK THREE*

_STORY AND WRITING BY_
_©JAMEEY YAR'MUTAN KANKIA❣️_

_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION_

_Ban yarda yan YouTube su daukar man labari su mai dashi audio ba tare da izini na ba!yin haka babban laifi ne idan kana bukata yi man magana kai tsaye! 08160508316_

https://chat.whatsapp.com/KBHTLLgPYd6Ir7V3PXpBGJ

*91-100*

Koda suka shigo cikin gidan cizewa Jidda tayi tana kallon Ammie sai kuma ta rushe da kuka tana girgiza kai tace.."Ammie ba zan iya ba, i'cant ba zan iya shiga cikin gidan ba,nasan ko na shiga koroni Baba zai yi kuma ga dukan alamu yana gidan tunda yau weekend Dan Allah Ammie kiyi man rai mu koma karda mu shiga nidai tsoro nike ji."
Dakatawa Ammie tayi da yake daga Jidda sai ita suka shiga cikin gidan su kuma su AK suna tsaye kofar gida dan sai an basu izini zasu shigo...kallon Jiddarh Ammie tayi tana cewa.."haba mana Daughter karda kiyi haka please kiyi addu'a sannan kuma ki sama kanki dauriya da juriyar komai zaki tarar a gidan nan but Ina son na Kara tuna maki duk tsanani yana tare da sauki fa.

And kowa da tashi qaddara ke haka taki qaddarar take,kuma in shaa Allah Ina gaya maki komai zai zo da sauki ba abunda zai faru sai alkhari Jiddarh kwantar da hankalinki please." gyade mata kai kawai Jiddarh tayi sai kuma ta share hawayenta tana tafiya jikinta sai karma yake tana 'bari tana mazari kattttt haka take.
Bakin kofar da zata sadasu da parlo suka tsaya suna yin nocking,sai da sukayi sau biyu ana ukkun ne aka zo aka bude...wata yarinyace da bata wuce shekara 7 ba tazo ta bude kofar,Koda ta bude tsaye tayi tana kallonsu Jidda daga can cikin gida suka ji ana cewa.

"Wai Nana waye ne yana nocking kuma ba kije kin bude ba zaki bar mutun a tsaye.?"

Yarinyar da aka kira da Nana ta turo baki gaba cikin shagwaba tace..."Mama na bude fa wasu ne.".."okay kuma ba zaki shigo da su ba, shiyasa Dejarh ta fiki iya tarbar bak'i fa." Yanda Nana take sunburo baki zaka gane an shagwabe yarinyar ba sai an gaya maka ba,kuma kallo d'aya zaka yi mata ka san tana cikin hutu da jindadi tana samun kulawa ta mussaman.

Murmushi Ammie tayi tana cewa.." sannu yanmata." Ita dai Nana dan murmushi tayi tana cewa."ku shigo." murmushi Jidda tayi tana bin yarinyar da kallo,yanda ta girma ga kuma kyaun da Allah ya bata har ya zarta wanda ta san ta da shi...shiga suka yi suka samu waje suka zauna,ita dai Jidda a sanyaye take suna dai Zaune sai ga wata yarinyar ta fito tsawansu d'aya da ta farko.kuma kamarsu d'aya tana fitowa ta kalli su Jidda sai ta washe baki tana cewa.

"Sannunku da zuwa." K'arasa isowa tayi gabansu tana kallon Jidda sai da tayi minti biyar tana kallon Jidda sai ta saka yatsanta a cikin dimples dinta tana cewa.

"Kina da kyau Ina son dimples dinki irin nawa."

Murmushi kawai Jidda tayi tana yin kasa da kanta sai goge hawaye take,maida kallonta wajen Ammie tayi tana cewa.."Kema kina da kyau." Shafa kanta Ammie tayi tana cewa."Allah yayi maki albarka." Dariya Dejarh tayi tana barin wajen direct kitchen ta nufa tana cewa..'Mama ki zo kiga wasu masu kyau a parlo." K'arasa juye abincin tayi a cikin warmers tana kallon Dejarh tana murmushi tace.

"Saurin da nike kenan na fito naga su waye Dejarh,maza dauke warmers din ki fara Kai su dinning kafin Babanku ya dawo ko.?" dariya yarinyar tayi tana fitowa daga kitchen tace.."Mama tace ga tanan fitowa ku dan K'ara hakuri." Sai kuma ta kalli Nana tana cewa.."Nana ki taso mu ida kwaso kayan mu kawo dinning." Tashi Nana tayi tana shiga kitchen dan taimakawa yar'uwarta.

Anan Jidda ta k'ara banbance Nana da Dejarh ita Nana miskilace sab'anin ita Dejarh da take da son mutane da kuma yawan magana,bayan sun gama jera dinning din suka dawo parlo suna duba homework din su kwabe fuska Nana tayi tana cewa.

DA'IMAN ABADAN (ZAZZAFAR KAUNA)Where stories live. Discover now