ZAZZAFAR KAUNA 181-190

216 9 17
                                    

*🌺DA'IMAN ABADAN*🌺
_ZAZZAFAR KAUNA_
*~HOT LOVE AND FATE STORY~*

*BOOK THREE*

_STORY AND WRITING BY_
_©JAMEEY YAR'MUTAN KANKIA❣️_

_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION_

_Ban yarda yan YouTube su daukar man labari su mai dashi audio ba tare da izini na ba!yin haka babban laifi ne idan kana bukata yi man magana kai tsaye! 08160508316_

https://chat.whatsapp.com/KBHTLLgPYd6Ir7V3PXpBGJ

*181-190*

Driving yake amman hankalinshi yana wajenta ganin sam bata cikin happy sai yaji shima dai ga shi nan dai,dan a rayuwarshi abunda ya tsana shine yaga Zulaihat cikin damuwa ko kadan ne shima yana kasancewa a cikin damuwar kuwa...kasa shareta yayi har sai da yayi gyaran murya a hankali yace.."what wrong.?" Kamar jira sai ta fara hawaye kamar an kunna famfo,dafa kan shi yayi yana cewa.."Ya Salam." Gangarawa yayi bakin titi yayi parking yana kashe motar ya kamo hannunta yana murzawa a hankali a hankali yana hura mata iska a fuska sun kusa minti goma a haka sanann tayi shuru share mata hawayen yayi yana langwabar da Kai yace.."Tell me maiye damuwarki.?" Murmushi ta sakar mashi tana girgiza mashi Kai tace.."bakomai Kai na ne kawai take ciwo." Take ya k'ara shiga damuwa dan ji yayi da yana da yanda zaiyi da ya maido da ciwon kan a kan shi ya bar mashi matarshi dan bai son yaji ko wani ciwo ya hauta.

Sannu yayi mata a cikin damuwa yana yi ma motar key suka tafi..suna isa gida da kan shi ya zagaya ya bude mata kofa ta fito ya kulle ko laptop din shi bai dauka ba dan a rude yake da ciwon kan da tace mashi tana yi,kama hannunta yayi suka nufi gida suna shiga ya zaunar da ita saman kujara ya cire mata hijab din ta har da dankwalin ma wai suna Kara mata wani ciwon ai...ita dai kallonshi kawai take tana mamaki kamar ba shi ba,wai ita yau Najeeb yake nuna ma kula harda damuwa dan tace mashi kanta yana ciwo just ciwon kai fa tace ba wani ciwon ba na daban Allah kenan.

Bayan ya cire mata ya kwantar da ita saman kujerar tana ra'da mata sorry a hankali ya wuce kitchen custard ya had'a mata wanda yaji madara but bai cika mata sugar ba sosai a cikin bcox shi bai shiri da sugar sam bai ma iya zuba shi ba ko kadan.

Sandwich yayi mata sharp sharp ya fito ya ajiye a gabanta ya koma ya dauko ruwa da lemu ya ajiye ya koma room din shi ya dauki first-aid box ya ajiye sanann ya d'ago ta yana cewa..."Oya tashi ki fara cin abinci sai ki sha magani ko." Shagwabe mashi tayi tana wani k'ara lafewa jikinshi tace.."oooo Huby ni ban son magani fa Allah ko."

Lumshe idonshi yayi yana saukewa a kanta sai kuma Shima ya samu kan shi da yayi mata shagwabar yana cewa.."Ayya!sorry adan kadan zan baki maganin ban son ciwon ya wahalar man da ke that why."

Turo baki tayi tana k'ara kwantawa saman shi tana lumshe idonta, murmushi yayi yana d'ago ta yana cewa.."okay bari na baki da kaina hakan yayi ko.?" Hawaye ta fara yi tana cewa.."ban jin yunwa fa." Zaunar da ita yayi saman cinyarshi yana cewa.."kukanan naki yana wahalar dani sosai,dan Allah ki daina yana ba zuciyata wahala gane wa ne baki yi stop it please."

Share mata hawayen yayi yana b'ata abincin a hankali sai wani shagwabe mashi take tana wani lafe mashi..shi kuwa daurewa kawai yake dan yanda take lefe mashi ba Karamin harzuk'ashi take ba, daurewa kawai yayi yana k'ara control din kan shi.

Bayan ya gama bata abincin sai da sukayi daru sosai sannan ta sha maganin ya taimaka mata ya raka ta har bakin room dinta sai dai bai shiga ba,daga bakin kofa ya tsaya yana jaijada mata akan tayi wanka sai ta kwanta Allah ya k'ara sauki ya juya ya tafiyarshi.

Ba iya nan taso ya tsaya ba taso ya rakota har cikin room din, kuma ya zauna yaita yi mata sannu ya shirya mata da kan shi tun da ai tace mashi bata lafiya..kwanciya tayi tana tunanin hanyar da zata bullo kuma wanda zata k'ara samun kusanci da shi fiye da wannan ma.

DA'IMAN ABADAN (ZAZZAFAR KAUNA)Where stories live. Discover now