ZAZZAFAR KAUNA 231-240

158 4 0
                                    

*🌺DA'IMAN ABADAN*🌺
        _ZAZZAFAR KAUNA_
*~HOT LOVE AND FATE STORY~*

*BOOK THREE*

_STORY AND WRITING BY_
_©JAMEEY YAR'MUTAN KANKIA❣️_

_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION_

_Ban yarda yan YouTube su daukar man labari su mai dashi audio ba tare da izini na ba!yin haka babban laifi ne idan kana bukata yi man magana kai tsaye! 08160508316_

https://chat.whatsapp.com/KBHTLLgPYd6Ir7V3PXpBGJ

*231-240*

"Kai ni dallah can matsa ka ban waje,ni banga amfaninka a wajen nan ba Najibu." tsaki tayi tana nad'e carpet din sallah tana cigaba da cewa.."Ina dalili yaran yanzun baku da kunya da kawaici wallahi,sai kace ce maka akayi mutuwa tayi zaka wani kama yi mana wannan rurudu..maza ka dauki matarka ku bar man waje ba zan iya wanann rashin ta idon ba nikam..daukarta ka maidata can shashen uwarka sai kaje ku karata a can amman na anan ba karma aja man sheri ina zamana cikin rufin asirin Allah."

Rasa abun ce mata ma yayi sai kama hannun Zulaihat da yayi tana kureta da ido tausayinta ya kama shi maike damunta tambayar da yake ma kan shi kenan,yasan lafiya lau ta bar gida tazo gidansu da cewa yayi ta tsaya yayi dropping dinta tace aa da motarta zata tafi tun da ta iya driving din nan itama dai ta hutar da shi ya tafi wajen aikinshi.

Har abinci sai da ta bashi yaci ya koshi da kanta ta shiryashi ta raka shi har bakin mota ta bishi da kiss and hunging sannan ya tafi ya za'ayi ya dawo kuma ya tadda bata lafiya dan ya tambaya ya zama laifi,tsaki Hajja tayi tana nuna mashi kofa tace.

"Ka dauketa nace ku barman gida,ni bansan jan sheri da neman bala'i daman Ina zaman zamana suka shigo man kuma ko ruwan gidana yau bata sha ba balle ace wani abu tasha a ci ahtoh ni ban son jan sheri da neman masifa dan haka a fice man daga gida kuma karda a sake a kama sunana."

Hawaye ta kama matsewa tana cewa.."Allah sai ya sakaman nikam Ladi duk wanda ya kama sunana a ciwon matar wanann marar mutuncin,sai nayi shara'a da duk wanda ya kama sunana dan hukuma ce zata rabamu da shi dan ba ruwana nidai akan hak'ina sai inda karfina ya kare,dan haka tun wuri kusan inda zaku ce ta fara cutarta amman ba dai nan ba."

Cikin kuka ta cigaba da cewa.."kuma wallahi kunji dai na rintse duk wanda yace a gida wannan matar tayi amai ban yafe ba kuma sai Hamisu ya shiga tsakani na daku ko kuma ba bar maku gidanku na koma wudil..na koma inda aka san mutuncina da kuma martaba ta ba zan zauna nan ba wanann marar mutuncin ya tisani gaba da tambayoyi akan matarshi bayan ni ko ruwan gida bata sha ba balle ace."

Ganin yanda take kuka bilhaki da gaskiya yasa Yaya Seemarh tashi ta koma hannunta ta zaunar da ita cikin kwantar da murya Yaya Teemarh tace.."haba Hajja kukan namaiye kike haka.?" K'ara rushewa da wani sabon kukan tayi  tana girgiza kai hadi da fashe majina tace.."bari Simatu barni nayi maganata ai gaskiya ce idan tazo dole a fadeta..ba yanda za'ayi a kama sunana a cikin wanann maganar ai dole na tashi tsaye sai inda karfina ya k'are dan ba zan duba Ido ba ina kallo ayi man sheri ba zan yarda ba."

Girgiza kai Yaya Seemarh tayi tana guntse dariyarta dan tana ma su Khadi warning da Ido da tuni sun fara dariyarsu sanin hali sanin wacece Hajja yasa suka kama hadiye dariyar tasu dan neman zaman lafiya...cikin kwantar da murya Yaya Seemarh tace.."haba Hajja ai ba wanda zai kama sunanki mai ma kikayi da har za'a kama sunanki?nidai ai bamu ga abunda kikayi ba,keda akayi ma laifi ma akayi maki amai a gida kuma kikayi hakuri ai godiya ma za'ayi maki amman ba wanda zai kama sunanki,Kinga ma bacci take idan ta tashi sai su tafi gida ko kuma ya kaita asibiti."

Share hawayenta Hajja ta kamayi tana cewa.."naji nidai ya tadata su bar man gida karda su sake dawo man Simatu,baki ga irin kallon da wanann marar mutuncin yake man ba shiyasa." Kuka ta cigaba da shi tana cewa.."haba abun da ciwo sosai da sosai kamarni Najibu yake ma kallon banza akan matarshi,duk wahalar da na sha dashi a banza ai nasan da Murjanatu ce ba zai mata kallon banza ba ko kuma Zainab da yake nice ya raina ma wayyo yake man kallon banza..to bari Kabir yazo sai yaji abunda akayi ma uwarshi yau a gidan nan bakin su tafi dai dole a zauna a bi man hak'ina ko kuma na Kai mutun a hukuma a anso man hak'ina dan akan hak'ina ba abunda ba zan yi ba."

DA'IMAN ABADAN (ZAZZAFAR KAUNA)Where stories live. Discover now