ZAZZAFAR KAUNA 131-140

167 6 5
                                    

*🌺DA'IMAN ABADAN*🌺
        _ZAZZAFAR KAUNA_
*~HOT LOVE AND FATE STORY~*

*BOOK THREE*

_STORY AND WRITING BY_
_©JAMEEY YAR'MUTAN KANKIA❣️_

_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION_

_Ban yarda yan YouTube su daukar man labari su mai dashi audio ba tare da izini na ba!yin haka babban laifi ne idan kana bukata yi man magana kai tsaye! 08160508316_

https://chat.whatsapp.com/KBHTLLgPYd6Ir7V3PXpBGJ

*Comment section kuna chnza man ra'ay fa🧐,sharhinku yasa na gantale yi yin posting during weekends ko hutun ma bamuyi ba wai mai ya faru ne😱🫣*

*131-140*

"Baba Bishir." Sai kuma yayi shuru yana maida kan shi k'asa yana sosawa a hankali,hawaye ne kawai yaji suna zubo mashi ya zai yi da rayuwarshi?tabbas ba zai iya rayuwa babu Jidda ba kuma yana sane da irin kallon tsanar da take mashi..ya cancanci haka daga gareta amman yana son ta sake bashi dama a karo na biyu,yana son tayi mashi uzuri akan abunda yayi mata a baya,sonta da kishinta ne suka rufe mashi ido har ya aikata abunda ya aikata.
Baba Bishir ne yayi magana yana cewa.."Haidar ya ka kira sunana kuma kayi shuru? Yi maganarka kofa a bude take nan wajen zaman sulhu ne da fahimtar juna ya kawo mu dan haka ba kai ba duk wanda yake da magana yayi maganarshi."

Share hawayenshi yayi dan ya rasa ta ina ma zai fara,amman yaji zai dauki duk wani wulakanci da cin mutuncin da duk zatayi mashi ba ita ba Koda kuwa su Bash ne bama kamar Bash yasan waye Bash a wajen zuciya,zai jure zai dauka fatan shi ta zama mallakinshi ya kuma rayu da ita *DA'IMAN ABADAN* ya nuna mata irin *ZAZZAFIYAR KAUNAR* da yake mata furzar da iskan bakinshi yayi yana kallon Baba Bishir yace."Baba daman so nike a k'ara bani dama a karo na biyu Ina son na auri Jidda dan na k'ara gyara zumincin da nayi *SANADIN* b'atawa, tabbas nasan ban cancanci haka daga gareku ba duba da irin abunda nayi amman duk da haka karda a kalli laifina a dai sake bani damar na gwada sa'a ta."

Tunda ya fara maganar AK yake kallonshi yana jin gabanshi yana faduwa,daman abunda ya guda kenan karda  ta dawo Haidar ya sake shigowa da bukatar aurenta,yana tsoron karda itama Jidda din ta amince da bukatar Haidar duba da *SANADIN SHI* ta bar gidan su,sanadin son shi ne silar shigarta duniya.. d'ago kanshi yayi yana saukewa saman fuskar Jidda da ta kura mashi ido tana sakar mashi murmushi kalar tausayi yayi mata tana dan kwabe fuska,turo baki tayi tana nuna mashi karda ya damu ita din ta shi ce, murmushi yayi mata yana sauraren Baba Bishir yaji mai zai ce akan maganar Haidar din.

Rintse idonshi Haidar yayi yana budewa gami da furzar da iska mai zafi a bakinshi,dan komai sukayi akan idon shine mai hakan kenan nufi?kar dai ace soyayya take da wannan guy din duba da irin kallon da yake mata, itama ga yanda take wani shagwabe mashi fuska, inalillahi yayi a zuciyarshi yana jin jikinshi yayi sanyi dan alamu sun nuna ba ma zai samu karbuwa a karo na biyu ba a wajen Jidda.

Murmushi Baba Bishir yayi yana cewa.."wanann kuma ai ba humurunmu bane Haidar wannan maganar tsakaninka da Jidda ne,kasan dai  mu bamuyi ma yaranmu auren dole balle kuma Jidda ba yarinya bace tasan abunda ke mata ciwo zata iya zab'a ma kanta mijin da take so take son rayuwa da shi *DA'IMAN ABADAN* dan haka idan kun sasanta kanku bamu da matsala idan kuma baku sasanta ba kuma sai ayi hakuri a rungumi qaddara."

D'aga Kai kawai Haidar yayi yana godiya yana da gudurin tinkarar Jidda komai zata yi mashi kuwa zai sanye har sai yaga ta zama matar shi... addu'a akayi kowa ya kama gaban shi duk da Haidar yaso yayi magana da Jidda amman bata bashi fuska ba sai dai yayi hakuri ya bar gidan akan zai dawo washe gari.

★★

*ABUJA 🥀*

D'ago shi Moha yayi yana kallon shi sai kuma ya hau share mashi hawayen yana mamakin kalar abun da yasa Najeeb kuka,kuka fa kuka wannan na hawaye rabon da yaga hawayen Najeeb tun rasu Baffah ,amman yau ga Najeeb nan yana kuka har da hawaye hawaye sosai ba kadan ba.
Bai hana shi ba amman yana dan bubbuga mashi bayan shi har yayi shuru yana sauke ajiyar zuciya sai kuma ya kalli Moha yana cewa.

DA'IMAN ABADAN (ZAZZAFAR KAUNA)Where stories live. Discover now