45

1.6K 341 224
                                    

SADIQ POV.

Rayuwar farincikin da Ummi a yanzu, ta mantar da shi duk wani farincikin rai da damuwa da yake ciki ciki kuwa har da wacce Zinneera ta saka mishi, Mama ba laifi tana son Ummi domin ta yaba da hankalinta da yadda take nuna musu kulawa ga alheri abun hannunta be taba tsone mata ido ba.
  Wani lokacin yana tasowa daga aiki zata shirya masa abincin tun daga gidan mahaifinta ta aiko masa, ko ta aikowa Mama. Idan yaje fira kuma har cikin falon mahaifinta yake zama suyi firar ta gabatar da gurin mahaifinta suna gaisawa yafi a kirga.

Yau ma sauri yake ta yi saboda Ummi ta fada masa cewar yau akwai surprise, he don't know what it's that's why yake jin kamar ma ya bar gurin aikin ya koma gida, domin ta fada masa a gida surprise din yake, daga baya ya fara tunanin ko abinci ne ta aje masa ko kuma wani abun na kawa ko na ci. Biyu saura kwata ya tashi office sai ya bi ta gidan mai dan karawa motarsa man da yake tunanin ba zai kaishi gida ba. Ya tararda layi kasancewar NNPC ne farshinsu ya dauka kadan dana sauran gidajen mai shiyasa ake musu taro sosai.
Yana cikin motar ya hango abokinsa Husaini yana dago masa hannu, sai ya ciro wayarsa ya kira shi.

“Husaini ya?”

“Daidai ya aikin?”

“Alhamdulillah”

“Ya Zinneerar mu”

“Kai ba wannan maganar”

“Kamar ya?”

“Kai dai bari kawai”

“Ban gane ba? Taya zaka ce ba maganar ka yafe ta ne?”

“Ai dole na yafe, kai da bari na sha ma zamu yi maganar”

Daga haka ta kashe wayar, Husaini na gabanshi a dayan layin dan haka ya rigashi shan mai sannan aka kawo kansa shima aka zuba masa na kudinsa ya wuce. Be lura da Husainin gefen titin fake da motarsa ba har sai da yai masa horn, sai ya faka tasa motar gaban ta Husaini ta fito ya nufo Husaini yana murmushi.

“Kar dai ka ce min Sadam ya fi karfinka”

Husaini ya fada yana bude motarsa ya fito, sai Sadiq ya mika masa hannu suka tabe yana kyalkyal dariya.

“Ba karfina ya fi ba, shima ai ya rasa ta kuma saboda ni”

“Ban gane ba”

A nan Sadiq ya labarta masa abunda ya faru da kuma kudinsa na aurenta indai gar Sadam be kai ga jikinta, da kuma dalilin fasawarsa saboda cikin da take dauke da shi, ciki har da labarin Ummi wacce yake so yanzu, da can Husaini yana ganinta a gurinsa lokacin da yake kwance asibiti idan yaje ganinsa, sai dai a zatonsa yar'uwarsa ce musamman yadda yaga tana da hidima da shi.

“Amman gaskiya Sadiq ka bani kunya, ga yarinya ka samu a bagas, aurenta ya mutu sai kuma ka ce wai ba zaka aureta dan tana da ciki ba? To ai shi Sadam din zai iya maida aurensa kuma kaga ita zatai maka kallon mayaudari”

“Husaini ciki fa nace maka tana da shi”

“To miye dan tana da ciki? Ba sai a zubar ba, kai da ba ka cika burinka na aurenta ba, kuma Sadam zai ji bakinciki idan ka aureta musamman ka zubar da cikin nan”

“No Husaini ni ba zan iya auren mace da wani namijin ya rigani kusantarta ba, ba zan iya auren matar wani ba matukar ya kai ga jikinta”

“Oh kai duk son da kake ma Zinneera na jikinta ne? Daman can ba saboda Allah kake son ta ba? Ai da nasan haka ne da ban baka shawarar ka ashe mata aure ba, nayi zaton son Allah ne shiyasa na ji haushi lokacin da Sadam ya aureta ya barka bayan kai ka shekara hudu tare da ita, kayi wa kanka adalci Sadiq be kamata yarinyar nan ta kashe aurenta saboda kai ba kuma ka gujeta, indai dan ta cikine ka same ta ku sasanta kanku sai a zubar kamin yai kwari”

ZABIN RAIWhere stories live. Discover now