CHAPTER 13

76 14 0
                                    

Yanzu mama ta San da tanimu,Dan yanzu daga labarin wurin lesson Sai labarin tanimu soyayya mukeyi sosai Ni da shi.
Ina daga kwance nake amsa wasu past question din jamb a wayata , vibrating naji wayar tawa tana yi na kalla Naga sunan CUPID murmushi nayi sannan nayi saurin dagawa Ina lumshe Ido na cike da doki na gaida shi,da tsokanar shi yanda ya Saba yake amsani,yace toh ya queen dina,ce Masa nayi lafiya,yace naji shiru baa nemeni bane me aka samu,ce Masa nayi karatu nakeyi,yace toh na Miki uzuri tunda karatu ne,tanimu nason karatu sosai indai zancen school ne he supports me sosai baya yarda nayi Wasa,
ba school ba ma kawai komai Yana kulani sosai,Yana min Kamar kanwarsa hakan yasa na ke Kara kaunarsa a zuciyata,ga Kuma biyemin duk shirmena,dawowa Dani yayi daga tunanin da nakeyi yayi yace toh Zan zo ganin mama ta anjima,nace oh mama kawai ma zaka Zo gani Banda Ni,dariya yayi yace eh mama kawai Banda ke,
ce Masa nayi tafi munyi fada na turo Baki kamar Yana gani na,karka Kara min magana,dariya ya kyalkyale yace toh kiyi hakuri,cewa nayi ban hakura ba,Sai yace toh Nima ki biyani wayata da Kika fasa ban manta ba🤣,hakuri nabashi nace toh na hakura,dariyar ya Kara Yi yace Kinga Sai dariya nakeyi a titi nazo shagon jamilu ne abokina Mai dinki,nace to kagaida shi ,sallama mukayi ya kashe wayar inata murmushi.
         Mama naje nafada ma yace zaizo anjima,zobo siyama ta hada yayi dadi kuwa sosai,na idar da sallar magrib na yafa gele rigar jikina na fito parlor,siyama ce ta bini da kallo, nace lafiya da wannan kallon malama,cewa tayi yayah Dan Allah da wannan kayan zaa Zo a ganki,kallon jikina nayi alaman Banga me yayi ba,buba ce ta atampa a jikina,mama tace gwara dai kifada Mata kwana biyun nan narasa meyasa Bata son sa kayan ta na arziki,gashi ma yau da zatayi bako,kunya naji kawai sai na koma daki na hau dube dube gashi narasa da wani kayan Zan chanza,Ina cikin dube duben wayata tafara ringing cupid nagani,Ashe har ya kirani sau uku kenan,Ina dauka yace toh kina nan kina min kwalliya ne queen dina?karki damu ai ke da kwalliyar ki aka haifo ki,Ina kofar gida duk yafada a tare,ya kulle min Baki da surutun shi cemasa nayi toh gani nan zuwa.
Yana kashe wayar na kwalla ma siyama kira ce Mata nayi tazo ta tayani duba kayan da zansa gashi har yacemin yazo tun dazu,dariya sosai siyama takeyi,tace wallahi yayah kina son wannan tanimu din Kinga duk kin rude,harararta nayi a hakan dai ta Nemo min wata lace peach harda daura min Dan kwali sannan na yafe veil white,nidai gaba daya ba Jin gayun nakeyi ba,Amma ya na iya siyama tazama Yaya ta🤣.Ina fitowa mama tace ko kefa,wucewa nayi nidai.
kofa na bude Masa ya shigo cikin gida,tunda ya shigo idonsa ke kaina,yi nayi kaman bansan Yana kallo na ba nagaida shi ya amsa da faraar shi sosai,yace Yan Mata na kinyi kyau sosai,gaskiya nidai nayi saa,Bari inzo inyi sauri kafin wani ya rigani,irin wannan kyau haka in kina fita zaa samu matsala,dariya yabani har zanyi magana Kuma Sai nayi shiru,yace toh ba magana ne kuma Ni dadina da ke a waya ki cikamin kunne innazo ki kasa magana,Sai a lokacin nace ai kace mama kazo gani dama ba Ni ba,yace toh yanzu gaskiya harda ke Dan wannan kyau haka,kulle fuska nayi da hannu na,nace toh muje wurin maman,ledar hannun shi ya Miko min sannan na shiga gaba Ina tafiya inajin kunya Dan nasan kallo na yakeyi,sallama nayi nashiga mama ta amsa,nace Mata yazo Sai tace Bismillah ya shigo,shigowa yayi ya tsugunna har kasa sannan ya gaida mama,mama ce Masa takeyi ya zauna Mana a kujera Amma Ina ya zauna ma a kasa abinsa,haka dai na wuce ciki nidai sun danyi fira da mama,sannan siyama ma tazo suka gaisa ta kawo Masa zobon,sannan mama tashiga ciki siyama ma tabita suka koroni parlorn.
  Munyi fira sosai ya nuna min Yan gidan su a wayar sa,mun fahimci juna sosai sannan yayi min alkawarin ganin baba soon duk da bashida aiki Mai karfi yanzu,na yarda da hakan tunda dai Nima Ina son sa,Kuma gashi   a hakan ma Yana aiki a wani private organization Kuma suna biyan sa ga kuma kasuwancin da yake taya baban sa,hanci na ya ja min wai zai shafamin mura da yakeyi,matsar da fuska ta nayi nace Kar ya shafa min,dariya yayi yace toh mura ta fa ni baa dauka,gashi Bata Jin magani,dariya dai nayi nace baka Sha peppersoup ba da ka warke ai,dariya yayi fada ma mama Zan tafi,
tashi nayi nafada ma mama zai wuce sannan na nuna Mata ledar da ya kawo,da tafito sukayi sallama sannan tace munga dawainiya Allah ya saka da alkairi agaida mutanen gida,a haka muka fito tsakar gida,ji nakeyi kamar Kar yatafi🙈.
har kofan gida na raka sa,ban Ankara ba naji ya kamo gemu na yadan daga fuska ta da nake kallon kasa na kalleshi,Sai ya manna min kiss a goshi na,yace ki kula da kanki,I love you Soo much,kunya naji sosai Dan Ni wannan abin sabo ne a wurina bantaba Jin kalanshi ba,kulle Ido nayi na wayance nace wallahi zaka shafamin mura,yace kinji ki ai,toh shikenan natafi,cewa nayi ya tsaya sannan nace mishi I love you too a hankali sannan nashigo gida na kulle kofa banji amsan shi ba.
Nashiga gida Ina murna sosai,Riga ce ya kawo min gown,Sai chocolates da turaren tsinke,dama yafada min turaren is for mama, chocolates for siyama,mama taji dadin firar su da shi,Sai tayita tambayana more about him duk nafada Mata,cewa tayi Wai zata fada ma baba,nace Ni nafiso yaganshi ne in yadawo karta fada tukunna,biyemin mama tayi Amma nasan saita fada ma baba yau dinann, Dan komai akayi Sai ta kwashe tafada ma baba ko da tace bazata fada Mai ba🤣.
Nashiga daki nayi sallar Isha Ina Kan sallaya Ina Jan charbi na naji ring wayata wa Zan gani Sai Yaya khalifa,da murnata na dauka nagaida shi,yace wato saidai inji labari wurin mama,nace Yaya khalifa labarin mene kenan,Wai ance an sa Miki Rana,kulle Baki nayi Ina zaro Ido kaman Yana gani na,ya kulle min Baki narasa ma me zance Masa,nace Yaya Wasa akeyi,wani ne fa daga zuwa yau ,dariya yayi yace to Haka dai siyama tafada min,nace dama Sai ita,labarin tanimu nabashi ,yay murna yace toh Allah tabbatar da alkairi,Inna dawo zaa Mana bincike akansa mugani,kunya naji mukayi sallama  nidai,Yaya khalifa yace dama Kuma nayi wata budurwa Inna dawo Zan Baki labari,nidai tsaida shi nayi nace yafada min wacece yaushe Kuma,kin fada min yayi,Wai saidai yadawo,Haka dai duk maita na na hakura nabarshi Bai fada min wacece ba.
Siyama na hango bakin kofan daki na,nace zakiyi bayani ne malama har kin Kai rahoto ko,ce min tayi saura Yaya batool yanzu zata kiraki itama,bin ta nayi da gudu itama ta ruga,kyaleta nayi nadawo daki abuna hafsa nakira muka danyi labari,nabata gist din abinda yafaru,mukayi sallama.
Tanimu yakirani muka Yi fira yanda muka Saba,yace min yafada ma maman shi about me yau,Kuma tayi murna zata fada ma baban su, Sai naji farin ciki a Raina,a hakan dai mukayita firar mu har bacci.
Please in kun karanta har nan kuyi min vote da comment,I will really appreciate,zai Kara motivating Dina,nagode.

NI DA YAN GIDAN MUKde žijí příběhy. Začni objevovat