page 3to4 &5 to 6

1.2K 56 1
                                    

[1/3, 10:17 AM] Hassana D'an Larabawa🥰: *TYPING*📲


💔👭 *HASSANA* 👭💔

                  *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣


*TARE DA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍



*page 5⃣to 6⃣*

WATTPAD:hassana3329

SADAUKARWA

*GAREKU Y'AN BIYU KYAUTAR ALLAH*

1- HASSAN TANKO ATK
2- HUSSAINI TANKO 80k

*ALLAH YASAKA MUKU DA ALKAIRI ABISA K'OK'ARINKU GAREMU NA POSTING ,SANNAN INA TAYAKU MURNAR KAMMALA LITTAFINKU ME SUNA K'AZAMA SHALELE ,HAK'IK'A KUNYI K'OK'ARI MATUK'A TWINS*


BARKAN MU DA JUMA'A Y'AN UWA ,ALLAH YABAMU ALBARKACIN WANNAN RANA ME ALBARKA 😍😍😍🙏🙏🙏







***Nasamu Baba yana sallamar wasu yara da suka zo sayen tumatur ,bayan ya sallame su ya tareni da fara'arsa yana fad'in "kyautar Allah har kundawo daga makarantar kenan ???shigo shigo ga benci ki zauna .

          Na shiga rumfar tasa ta langa langa da buhu inda yake zama Dan sana'arsa ,sana'ar da babu yanda Hamma sulaiman da Hamma Aminu da Adda Nabeela basuyi da Baba yadena taba ,tunda yanzu Allah yarufa musu asiri basu rasa komai ba ,amma Baba yak'i ,yace ba zai iya zaman gida ba yasaba da sana'arsa ,sukace ya sauya Sana'a nanma yak'i amincewa tilas suka barshi badon sun soba ,Hamma sulaiman yafi kowa jin haushin sana'ar nan ta Baba ,amma Baba baya kulawa yakance " sulaiman kenan wannan sana'ar da kake k'i yanzu da ita nayi maka komai har ka girma kazama haka kaida y'an uwanka .

            Na zauna kan bencin inayiwa Baba sannu ,ya amsa shima yana zama kusa dani ,na ajiye abincin ina fad'in "kayi hak'uri Baban mu bankawo abincin da wuri ba na barka da yunwa ko .....!?

"Baba yace " ai bana tare da yunwa me yawa ma ,d'azu nasha fura da nasiya a hannun wata Fillo ,ga kindirmo can ma a k'warya inzaki tafi kiwuce muku dashi gida ,akwai ragowar furar da Aminullahi yakawo jiya sai kudama kusha .....

  " Hassana tace "toh Baba Allah yak'ara maka bud'i na alkairi "


"Ameen, Ameen Hassanata" ,Baba ya furta yana k'ok'arin janyo butar dake gefensa domin wanke hannunsa ,da sauri na mik'o masa butar ya matsar da hannunsa gefe na zuba masa ya wanke hannun ,sannan yajawo abincin ya bud'e yana fad'in "nafison inci abinci da hannuna yafi albarka ,shiyasa bancika son saka cokali ba " nayi murmushi nace "hakan Nada kyau Baba "

         Bai dad'e da fara ci ba wata yarinya tazo sayen tattasai ,Baba yana k'ok'arin zare hannunsa Dan tashi yabata nace "Ah ah Baba yi zamanka kurum ,bari nazuba mata da kaina saina nuna maka idan yayi ko ???Baba yace " toh bismillah ,zuba nagani.

       Na karb'i kud'in yarinyar naira hamsin nazuba mata, nad'agoshi ina nunawa baba yagani ko yayi ?,Baba yace "d'an k'aramata wannan yayi tsada kyautar Allah " nace "toh Baba "na k'aramata nabata tatafi .



"Nadawo na zauna har ya kammala ci yayi hamdala ga sarki Allah ,yakuma wanke hannunsa ,da kaina nad'auki naira goma a cikin cinikinsa na tsallaka wani kanti nasayo masa pure water ,me kantin sai wani kallona yake yanamin murmushi da Sosa k'eya ,nayi maza na d'aure fuskata ina danasanin fitowa ba nik'ab a fuskata saboda yawan kallon da nakesha a gurin maza ma tamfar su cinyeni .

        Bayan Baba yagama shan ruwan sai ya d'akko nonon a k'warya yasa na d'akko bak'ar Leda na bud'e aka juye a ciki Dan yayimin sauk'in d'auka, tunda ga flask zan koma dashi gida shima , Baba ya sallameni ganin wasu masu siyan kayan miyar sunzo .

HASSANA DA HUSSAINA Unde poveștirile trăiesc. Descoperă acum