page13to14

642 40 0
                                    

*TYPING*📲


💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣




*TARE DA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍



*page 1⃣3⃣to1⃣4⃣*




WATTPAD :hassana3329


*TUNASARWA*👇

*MANZON ALLAH (S A W )YACE"WANDA YA KASANCE A ZUCIYAR SA AKWAI KWATANKWACIN KOMAYYA (ZARRA)NA GIRMAN KAI BAZAI SHIGA ALJANNA BA"*

*ABINDA AKE CEWA GIRMAN KAI SHINE TURE GASKIYA DA K'IN KARB'ANTA BAYAN MUTANE SUN SANTA,DA WULAK'ANTA MUTANE*

*AIKI ME FALALA*👇

*MANZON ALLAH( S A W)YACE " DUK WANDA YACE "SUBHANALLAHIL AZEEM WABI HAMDIHI"ZA'A SHUKA MASA BISHIYAR DABINO A GIDAN ALJANNA*



***Ko kad'an banyi niyyar amsa kiran ba saboda bancika d'aga kiran da ban San Numba ba ......sai dai nasamu kaina da son d'aga wayar a dai dai wannan lokaci .....bada b'ata lokaci ba kuwa na d'aga tare da karata a kunnena nayi cikakkiyar sallama ta addinin musulunci.

Daga can b'angaren aka amsamin sallamata tare da cewa "dafatan ina magana da HASSANA ne .... !? Jin muryar mace yasa nasamu nitsuwar amsawa sosai a hankali nace " eh itace ...dawa nake magana ...!?

           Maman sageer ce "aka amsamin ......nayi wal da ido da girmamawa tamkar ina gabanta nace " mamma barka da Safiya ,antashi lafiya ...!?lafiya lau daughter ya mutan gida da Hussainanki da yaro me wayo ....!?ta amsa da karsashi a muryarta .

Na juya na kalli sisina da taketa sharar bacci batasan me nake ba nace "gata tana bacci .....nima wayar ce ta tadani yanzu .....kowa yana lafiya " mamma tace "ayya sorry na tasheki a bacci ko ....!?wallahi nakasa jurewa ne dake na kwana a raina ......My daughter don Allah ina Neman alfarma a gareki gameda Muhammad sageer ......had'uwata dake da yadda komai ya wanzu akan idona jiya na tabbatar da zaki iya taimakona ...kuma zaki iya taimakawa sageer yafita daga rayuwar da yasaka kansa ciki .......sageer ba haka yake ba .....sageer yaro ne nagari .....sageer yanada hankali da tunani .....ba komai yasashi a wannan hali ba illah wata k'addara da ta gifta ..Wanda kuma nice SANADIN TA .....karkiga laifin sageer akan dukkan abinda yake aikatawa ....duk da bakisan komai ba amma inason kid'ora laifin a kaina ......idan zai yuwu inason mu had'u ni dake domin nabaki labarinmu da k'addarar da tasaka sageer a wannan yanayi ......"

Hassana tana sauraren mamma kanta na d'aurewa ....tunani take a ranta wane irin laifi mamma tayiwa sageer da har yafad'a wannan halin .....!?meyasa sageer yake ganin mata ba mutanen kirki bane ...!?meyasa yake gudun mahaifiyarsa kamar mutuwar sa .....!?menene acikin labarinsu ....!?duk wad'annan amsoshin suna gurin mamma itace zata warware komai ......"cikin ladabi Hassana tace "idan har kin aminta dani kibani labarinku ta Yaya ni zank'i amincewa na saurareki .....!?wallahi mamma na d'aukeki da daraja ,zan tsaya na saurari dukkan abinda zakizo dashi kodan samun maslaha .....wani Abu da baki saniba mamma tun randa nafara ganin Hamma sageer najishi a zuciyana tamakar jinina ....naji ina k'yamatar abinda yakeyi da burin ya daina .....gani d'aya nayi masa nasan mutumin kirki ne k'ila halin rayuwa ne yajefa shi a wannan halin ......mamma na amince ....ko yau kika shirya ni mai sauraronki ce ......kuma zan bada gudummawa wajen ganin komai ya dai dai ta insha Allah "

"Good bless u "thank u my daughter " mamma ta ambata da tsananin farinciki ...... Sannan taci gaba "idan babu damuwa zanzo har gidanku yau .....Dan na gaisa da ummanku ...sonake mu zama d'aya ....zamuzo tare da Nafeesa ......dafatan babu wata matsala .....!?

HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now