page 51 to 52

534 39 2
                                    

_________________________________

*TYPING*📲

💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣

*TAREDA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page5⃣1⃣to5⃣2⃣*

WATTPAD:hassana3329

® _PEN : WRITERS  ASSOCIATION_
_________________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~

https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/












*TUNASARWA*👇

HISABI

*ZA'A BIJIRO DA MUTANE SAHU SAHU GA UBANGIJINSU ,SAI YA NUNA MUSU AYYUKANSU ,YAKUMA TAMBAYESU GAME DA SU DA RAYUWARSU ,DA DUKIYOYINSU DA ILIMINSU DA ALK'AWURAN DA SUKA D'AUKA DA DUKKANIN NI'IMOMI ,JINSU DA GANINSU DA ZUKATANSU ,KAFIRAI DA MUNAFUKAI ZA'AYI MUSU HISABI AGABAN HALITTU DAN A WULAK'ANTASU ,KUMA A TSAYAR DA HUJJA AKANSU ,KUMA ASANYA MUTANE DA K'ASA DA YINI DA DARARE DA DUKIYA DA MALA'IKU DA GAB'B'AI SUYI SHAIDA AKANSU ,HAR SAI LAIFIN YA TABBATA SUN AMSA LAIFINSU ,MUMINI KUMA ALLAH ZAI KEB'ESHI YAGAYA MASA LAIFINSA HAR SAI YAZACI CEWA YA HALAKA ,SAI UBANGIJI YACE DASHI "NA SUTURTA MAKASU A DUNIYA KUMA NA GAFARTA MAKASU A YAU*
*KUMA FARKON WAD'ANDA ZA'A FARA YIWA HISABI SUNE AL'UMMAR ANNABI MUHAMMAD (S A W)KUMA FARKON AIKIN DA ZA'A FARA AUNAWA SHINE SALLAH DA KUMA JINI*






*AIKI ME FALALA*👇

*MANZON ALLAH (S A W )YACE *DUK WANDA YAYI SALLAH CIKIN YINI DA KUMA DARE SAU GOMA SHA BIYU ,ZA'A GINA MASA GIDA ACIKIN ALJANNA,RAKA'A HUD'U KAFIN SALLAR AZAHAR ,DA RAKA'A BIYU BAYANTA ,SANNAN KUMA RAKA'A BIYU BAYAN SALLAR MAGRIBA ,SANNAN RAKA'A BIYU BAYAN SALLAR ISHA'I ,SAI KUMA RAKA'A BIYU KAFIN SALLAR ASUBA*"






*SADAUKARWA GA DUK WANI D'AN GARIN GOMBE STATE ,ALLAH YASAKA MUKU DA ALKAIRI GOMBAWA ,HASSANA D'AN LARABAWA NA K'AUNARKU SOSAI DA SOSAI*🥰🥰🥰




*BARKANMU DA JUMA'A BABBAR RANA SISTERS ,ALLAH YABAMU ALBARKACIN WANNAN RANA ,INA GAISUWA GA MASOYANA*🤝🤝🤝








***Hamma Sageer yashiga tsananin tashin hankali da rud'iya a sanda yaji an d'aura aurensa da Hussaina,jikinsa yana makyarkyata yafad'a k'irjin Abdurrahman yanata juya kai ...yarasa inda zai tsoma ransa yaji dad'i ,wani irin tashin hankali yakeji yana d'awainiya dashi tamkar kansa zai juye ....

Yana rungume jikin Abdurrahman wani masifaffen amai ya yunk'uro masa ...take yafara kelayashi ajikin Abdurrahman tamkar zai amayar da y'ay'an hanjinsa ....gabad'aya mutanen dake wajen sukayo kansa sunayi masa sannu ....amai sosai yake shekawa hawaye na tsartuwa a fuskarsa ,Abdurrahman rik'e yake dashi duk jikinsu ya b'aci ,Hamma Aminu ne yazo ya janye Sageer daga jikin Abdurrahman ,sai Sageer d'in ya langab'e ajikin Aminu tamkar sumamme ,haka aka d'aukeshi zuwa gidan Aunty Nafeesa jikinsa zafi rau saboda zazzab'in da yakamashi a take ,,Mamma tayiwa doctor waya akan yazo ya duba Sageer ...kafin doctor yazo Hamma Aminu da Ya Abdurrahman sun gyarawa Sageer jikinsa Wanda idanunsa ke rufe amma hawaye basu bar gangarowa ba .Likita yana zuwa ya duba shi yasa masa drip yayi masa allurar barci ko Dan k'wak'walwar sa ta huta.

       
            A can gidama tunda Hussaina taji ance an d'aura aurenta da Hamma Sageer tafad'i sumammiya ,sai da Umma tadinga Shafa mata ruwa a fuska sannan ta farfad'o ,tunda ta farfad'o take wani irin kuka da surutai tarasa ina zata tsoma ranta taji sanyi ...mutuwar Hassana tadawo mata d'anya tamkar ranar da Hassanar ta rasu ,ba ita kad'aiba mutane da dama a ranar mutuwar d'anya ta dawo musu kowa saida yayi kuka, Hamma Sulaiman d'akinsu ya safwan yashige ya kwanta akan katifarsu yana zubda hawaye ,sakeena tabishi har cikin d'akin tasamu guri ta zauna dab dashi ,ganin hawayen da yakeyi sai tazame ta kwanta akan k'irjinsa ...inda taji zuciyarsa na tsananin bugawa ..itama hawayen yazubo mata har ya malala akan k'irjinsa ,a hankali tace "Abban sadauki " yanajin muryarta yasa hannu ya rungume matarsa, ya matseta a k'irjinsa yafashe da kuka yace "sakeenan Sulaiman daman haka mutuwa take da d'aci ....lallai duk Wanda bai San d'acin mutuwa ba toh ba'a tab'ayi masa bane ...iyalin gidanmu muntaso cikin farinciki da kyautatawa juna sakeena ...ko ina sha'awarmu akeyi ana kwatance da gidanmu ...amma yau mutuwa ta wargaza mana farincikin mu ...mutuwa tayi mana gib'i a zuri'ar mu .....mutuwa ta tafi da farincikin mu a wannan lokaci ....na rantse sakeenan Sulaiman bantab'a jin rayuwa tayi min K'unci kamar na wannan lokacin ba ....." Ya kuma fashewa da kuka .

HASSANA DA HUSSAINA Unde poveștirile trăiesc. Descoperă acum