page 59to60&61to62

648 42 3
                                    

[2/23, 2:15 PM] Hassana D'an Larabawa🥰: _________________________________

*TYPING*📲

💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣

*TAREDA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page5⃣9⃣to6⃣0⃣*

WATTPAD:hassana3329

® _PEN : WRITERS  ASSOCIATION_
_________________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~

https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/







*TUNASARWA*👇

ALJANNA

*ITACE MAKOMAR MUMINAI ,GININTA NA ZINARIYA NE DA AZURFA DA SIMINTI NA ALMISKI DA TSAKWANKWANI NA LU'U LU'U DA ZA'A FARANI ,TANADA K'OFOFI TAKWAS FAD'IN KOWACE K'OFA TAFIYAR KWANA UKU NE ,TANADA BAMBANCIN DARAJA D'ARI ,TSAKANIN KOWACE DARAJA DATA GABANTA KAMAR TSAKANIN SAMA DA K'ASA NE ,FIRDAUSI ITACE TAFI DARAJA DAGA NAN NE AKE B'UB'B'UGAR DA RUWAN TEKUNANTA ,AL'ARSHIN UBANGIJI YANA SAMANTA ,K'ORAMARTA TA ZUMACE DA NONO DA GIYA DA RUWA,K'ORAMUN SUNA GUDANA BA TARE DA RAMI BA ,MUMINI YANA GUDANAR DASU KAMAR YADDA YASO ,ABINCINTA DAWWAMAMME NE KUMA AN KUSANTO DASHI DON MASU TSINKA*

*zamu cigaba da bayyana dad'in aljanna a shafi nagaba da yardar Allah ,Allah yasa muna da rabon shiga cikinta*👆







*AIKI ME FALALA*👇

*MANZON ALLAH (S A W)YACE "DUK WANDA YAYI MA MAI CIWO JAJE ,TO ,YANADA IRIN LADANSA," BABU WANI MUMINI DA ZAIWA D'AN UWANSA JAJE A SABODA MASIFAR DA TA SAMESHI FACE ALLAH YA TUFATAR  DASHI DAGA CIKIN KAYAN ADO NA KARAMCI*






SADAUKARWA GA :

*AISHA ALIYU GARKUWA ,INA TAYAKI MURNAR KAMMALA LITTAFINKI ME SUNA (HUKUNCIN ALLAH)LALLAI WANNAN LITTAFI YA FAD'AKAR YA ZABURAR YA NISHAD'ANTAR KUMA YA TSAORATAR ,ALLAH YABAKI LADAN FAD'AKARWA YA YAFE KURA KURAN CIKI ,HASSANA D'AN LARABAWA NA TARE DAKE A KOYAUSHE*🥰🥰🥰🙏🙏🙏











****Ganin bata motsaba yasashi ambatar "inna lillahi wa inna ilaihir raji'un" a hankali kuma yad'ago fuskarsa daga kan tata sannan yayi hanzarin kunna famfon da ke gefensa yatari ruwa a hannunsa ya Shafa mata a fuskarta ,sai da yashafa mata sau uku sannan ta sauke ajiyar zuciya a hankali tana jujjuya idanunta .

             Kallonta yayi tana kwance kan cinyarsa yayinda yake zaune dafi'an a k'asan tayel d'in toilet d'in ,idanuwansu suka sark'e da juna alokacin da yake ambatar "sorry " ta D'an lumshe idanu hawaye na gangarowa tana kuma dafe cikinta dai dai cibiyarta ,ya fuskanci wajen na matsa mata da ciwo shiyasa yad'an ture hannunta yasa hannunsa gurin yad'an latsa da D'an k'arfi ,wani irin zillo tayi tana k'ara afkawa k'irjinsa hannunta rik'e da wuyansa tace "ahhhhh wayyo zafiiiiii" ya b'amb'are hannunta dake kan wuyansa ya maida hannun nata kan stomach d'inta yayinda ya aza nasa hannun kan nata yana shafawa yana sama da k'asa dashi zuwa gefe ,ya D'an kalleta sannan ya kawar da kai ganin yadda take wani mimmik'ewa ajikinsa saboda sak'on da hannunsa yake kaiwa ajikinta ,a hankali yace "wannan ciwon cikin da amai da kikeyi baya rasa nasaba da yunwa ,Hamma Sulaiman ya fad'amin bakya cin abinci sosai ...Dan haka kitashi muje ga abinci can kici....." Ta D'an girgiza kanta saboda takasa magana ,ya D'an d'aure fuskarsa shanyayyun idanunsa akan nata idanun yace "me kike nufi da girgiza kai ....!?taja wani irin numfashi ta furzar saboda yadda taji hannunsa ta saman rigar jikinta yana yawo dashi a ramin cibiyarta ,Wanda shi baima San yanayi ba ,cikin fizgo magana da kyarmar murya tace" zan.....zanyi .....zanyi amai ne idan naci abincin ......"hawaye na biyo kuncin ta .

HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now