page67to68&69to70

653 38 4
                                    

[3/1, 7:31 PM] Hassana D'an Larabawa🥰: _________________________________

*TYPING*📲

💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣

*TAREDA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page6⃣7⃣to6⃣8⃣*

Wattpad:hassana3329

® _PEN : WRITERS  ASSOCIATION_
_________________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~

https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/














*TUNASARWA*👇

CUTAR TALAKAWA DAGA MASU MULKI

*BABU WANI BAWAN ALLAH DA ZAI BASHI KIWON BAYINSA ,KUMA SAI A SAMESHI RANDA ZAI MUTU YANA MAI CUTAR DA MABIYANSA,FACE SAI ALLAH YA HARAMTA MASA SHIGA GIDAN ALJANNA*












*AIKI ME FALALA*👇

*MANZON ALLAH (S A W ) YACE "DUK WANDA YA LAZIMCI ISTIGFARI ALLAH ZAI SANYA MASA MAFITA DAGA KOWANE IRIN RINTSI ,KUMA DA FARINCIKI DAGA KOWACE DAMUWA KUMA YA AZURTASHI TA YADDA BAYA ZATO*







👇👇👇😂😂😂

*Amma Aunty Hassana kin shammacemu*😳😳😳
*Amma Aunty Hassana kin rud'amu*🙄🙄🙄
*Amma Aunty Hassana kin rikitamu*😭😭😭
*Amma Aunty Hassana kaza .....Amma Aunty Hassana kaza.......Amma Aunty Hassana kaza.....*

*kalaman da nayita cin karo dasu kenan a kowane group da na lek'a*😂😂😂👆

*HASASHEN MUTANE YANADA YAWA AKAN WANNAN LITTAFI NAWA TUN FARKON FARASHI ,AMMA BABU WANDA YA HASASO GASKIYAR ABINDA ZAI FARU ,READERS NA GANIN DUK WATA K'IYAYYA DA TAYI TSANANI TSAKANIN MACE DA NAMIJI TO K'ARSHE SOYAYYA TAKE ZAMA HAR AKAI GA AUREN JUNA ,ABINDA YASA SUKAYI TUNANIN ABINDA ZAI FARU KENAN ,SABODA YAWANCI ABINDA MARUBUTAN MU KE AMFANI DA SHI KENAN ,TOH KUNASO MUYITA MAI MAITA ABU D'AYA NE ,YAKAMATA ACE KOWACE MARUBUCIYA SALONTA YA DINGA SAUYAWA AKAN HAKA ,AKWAI HANYOYI DA DAMA DA ZAKA DAI DAITA ALAK'AR BA SAI AN KAI GA AUREN JUNA BA ,NAJI DAD'I K'WARAI DA KUKA FUSKANCI INDA NA DOSA HAR KUKETA YABAWA FASAHATA DA K'IRK'IRA TA ,BA WAYONA BANE KO DABARATA HAKAN BAIWACE DAGA ALLAH ,KUMA INA GODIYA GA RABBIL IZZATI ,MASU CEWA NA SASU KUKA SOSAI SUYI HAK'URI HAKA YANAYIN LABARINA YAKE ,KUMA TUNAWA DA MUTUWA WANI K'ARIN IMANI NE DA SAMUN LADA ,KUDAI KUCIGABA DA BINA KAWAI ,LABARAINA SUNA D'AUKE DA FAD'AKARWA ,NISHAD'ANTARWA ,ILIMANTARWA ,TAUSAYI ,SOYAYYA ,JIN K'AI ,ZUMUNCI ,BAN DARIYA ,DAMA SAURAN ABUBUWA,NICE TAKU D'INNAN DAI HASSANA D'AN LARABAWA*🥰🥰🥰🥰🥰






***Tamkar mahaukaciya haka take zare idanu tana duban mutanen da ke gabanta ,ta kuma runtse idanu tana dukan kanta da hannunta ....yayinda Hassana da Abdurrahman ke durk'ushe gabanta rik'e da hannayenta ,Umma kuma tana tsaye a Kansu idanunta akan Hussainar tana kallonta .


Cikin kid'ima Hassana take kallon yadda Hussaina ta firgice gabad'ayan ta ,girgiza hannunta tayi tana ambatar "sisina.....!
Hussaina ta k'urawa Hassana idanu kamar zata cinyeta sai uban gumi ne yake yanko mata amma takasa magana ,shima Abdurrahman tsananin mamaki da tsoro ne ya isheshi yarasa me yasamu Hussainar haka adai dai wannan lokacin,
Umma dake tsaye ta sunkuyo tana kallon Hussaina yayinda Hassana ta kai hannunta goshin Hussaina tana share mata zufar dake tsattsafowa ,Umma tace" ke Hussaina lafiyarki k'alau kuwa ....!?meke faruwa ne ....!?,
Hussaina tad'ago hannayenta tana Shafa fuskar Hassana zuwa jikinta sannan da k'yar ta fizgo magana a bakinta tace "Ummana ,da gaske Hassanata ce agabana ko kuma haukacewa nayi ne ....!?dukansu suka kalli junansu da mamaki a fuskokinsu ,sai Hassana ce ta katse mamakin nasu tadubi Hussaina da murmushi akan fuskarta tace" nice mana sisinah ...,wai anya lafiyarki kuwa ....!?Hussaina takuma runtse idanu murya na rawa tace "kece ...!?da gaske kece ....!?na rantse inajin na haukace kawai....!?
Abdurrahman ne ya kalli Umma yace " Umma ina Babangida ne .....!?
Umma tace "k'ila yana k'ofar gida ....menene...!?
Yad'an karkatar da kansa yace " a kirawoshi ya mintsini yarinyar nan ko zata nutsu ...tunda naga shi gwanine wajen iya mintsini ...."wani irin kallo Hussaina tabishi dashi yayinda shima ya k'ura mata ido yana D'an murmushi yad'agamata girarsa yace "ba sai kin furta ba nima nasan ba ganeni zaki yiba ,tunda kike tantama akan Hassanarki ai kuma duk duniya babu Wanda baza kiyi tantama a kansa ba ....!
Idanu Hussaina takuma rufewa k'wak'walwarta na wani irin nazari ,dukkansu k'ara zuba mata idanu sukayi wajen minti uku kafin tabud'e idanun a rikice tayi wata irin zabura ta afka jikin Hassana ta k'ank'ameta har suna shirin fad'uwa da sauri Umma ta tarosu .

HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now