page31to32&33to34

746 39 2
                                    

[1/26, 8:19 PM] Hassana D'an Larabawa🥰: _________________________________

*TYPING*📲

💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣

*TAREDA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page3⃣1⃣to3⃣2⃣*

WATTPAD:hassana3329

® _PEN : WRITERS  ASSOCIATION_
_________________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~

https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/




*AIKI ME FALALA*👇


*MANZON ALLAH (S A W) YACE "DUK WANDA YA TASHI DA DADDARE KUMA YA TASHI MATARSA ,SUKAYI SALLAH RAKA'A BIYU A TARE ,ZA'A RUBUTA SU DAGA CIKIN MASU AMBATON ALLAH DA YAWA MAZA DA MASU AMBATON ALLAH DA YAWA MATA*





*TUNASARWA*👇


*MANZON ALLAH (S A W)YACE "ALK'AWARIN DA KE TSAKANIN MU DASU (KAFIRAI) SHINE SALLAH ,DUK WANDA YA BARTA TO YA KAFIRTA ,KUMA YACE " TSAKANIN MUTUM DA SHIRKA ,BARIN SALLAH*






*INA YAWAN SAMUN TAMBAYA DAGA FANS WAI SHIN LABARIN HASSANA DA HUSSAINA LABARINA NE NIDA TAWA HUSSAINAR*??

AMSAR ITACE👇

*BA LABARINMU BANE BA KUMA TARIHIN MU BANE ,BABU MA ABINDA YAYI KAMA DA LABARINMU A LABARIN ,WANNAN K'IRK'IRARREN LABARI NE DABAN DA NUFIN FAD'AKAR DAKU DA NISHAD'ANTAR DAKU ,TARE DA SANIN DAD'IN ZUMUMCI A RAYUWA,DAFATAN KUN FAHIMTA MASOYANA ,ANA KYAWUN TARE TSAKANINA DAKU*🥰🥰🥰





****Hussaina tanasa kanta cikin soro Hamma sulaiman na shirin fitowa ,ta kauce tana gaisheshi ,ya amsa yana cewa "ke d'an biyoni cikin mota inbaki sak'o " yayi gaba abinsa .

           Tad'an bishi da ido tana tunanin wane sak'o kuma.....!? Har yashiga motar sannan tabishi itama ,ta bud'e wajen me zaman banza ta shiga ta zauna tace "gani Hamma " bai dubeta ba wayarsa a hannunsa yana daddannawa sai da ya d'auki lokaci sannan  yace "ni waye a gareki...!? Taji tambayar a bazata shiyasa ta d'ago kai tana kallonsa kawai batace komai ba ,idanunsa akan wayar yakuma cewa " kamar fa tambayarki nayi amma kikayi shiru kina kallona ,meyasa idan an tambayeku Abu bakwa bada amsa kai tsaye sai ku tsaya kallon mutum ...!?me kuke kallo a fuskata da Baku sanshi ba ne...!?Hussaina ta kawar da kanta daga kallonsa tana k'unshe dariya tace "sorry Hamma, kai d'in ai babban yaya nane, kuma magajin Uba agareni " yana jin tafad'i haka ya ajiye wayar kan cinyarsa yajuyo yana dubanta face to face yace "Ashe idan nanemi alfarma a wajenki zan iya samu kenan ...!?ta d'an sunkuyar da kai saboda yadda Hamman ya tsareta da idanu tace" kadai bani umarni kawai Hamma ,ai kafi k'arfin Neman alfarma a gurina ,ya d'an lumshe idanu yayi wani murmushi da baicika yin irinsa ba ganin tabashi babbar dama ,yace "so nake ki hak'ura da Abdurrahman ...kicireshi a zuciyarki ...kuma ki hak'ura da aurensa ..."

        A gigice ta d'ago kanta tana matsowa jikinsa kamar zata haye cinyarsa ,ta dafe k'irjinta wajen zuciyarta idanu a warwaje take kallonsa ,bakinta yana mugun rawa takasa magana sai girgiza kai takeyi hawaye yaciko idanunta ....ganin yadda tayi mugun razana hannunta ak'irjinta yasa Hamma sulaiman ya kalli hannun da ta dafe k'irjin yace "ya dai ...!?zuciyarki tayi ciwo ne saboda nace ki rabu da Abdurrahman ...!?hawaye ya kwararo idanunta da k'yar tayi magana tace" eh Hamma, bakaji yadda zuciya ta take bugawa ba wallahi ...."ya k'ara murmushi yace "kefa kikace nafi k'arfin alfarma agunki ...sai dai nabaki umarni ...Ashe bazaki iya bin umarnin ba kenan ....!?sai takuma matsowa ta d'ora kanta a kafad'arsa tana hawaye tace" kayi hak'uri Hamman mu ....ka sauya wani umarnin ,wallahi inason ya Abdurrahman ,bazan iya rabuwa dashi ba Hamma, ya d'an ture kanta yana fad'in "d'agani malama " ta d'aga masa kafad'ar amma kuma sai takama hannunsa ta rik'e ,hawaye nata ambaliya a fuskarta .

HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now