page45to46&47to48

676 39 9
                                    

[2/6, 11:48 AM] Hassana D'an Larabawa🥰: _________________________________

*TYPING*📲

💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣

*TAREDA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page4⃣5⃣to4⃣6⃣*

WATTPAD:hassana3329

® _PEN : WRITERS  ASSOCIATION_
_________________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~

https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/








*TUNASARWA*👇

SIRAD'I

*WATA GADA CE DA TAKE SHIMFID'E AKAN WUTAR JAHANNAMA DOMIN MUMINAI SU GIFTA TA KANTA ZUWA ALJANNA ,MANZON ALLAH (S A W) YA SIFFANTA SHI DA CEWA "YAFI GASHI SIRANTA ... KUMA YAFI TAKOBI KAIFI" MUSLIM NE YA RAWAITOSHI*



*AIKI ME FALALA*👇

*MANZON ALLAH (S A W) YACE"WANDA YA ROK'I ALLAH MUTUWAR SHAHADA BISA GASKIYA,TO ALLAH ZAI BASHI MATSAYIN SHAHIDI KODA KUWA YA MUTU NE A BISA SHIMFID'AR SA*



*KULLU NAFSIN ZA'IK'ATUL MAUT*
🙏🙏🙏🙏🙏🙏






         Wani irin zazzafan hawaye ya zubowa Baba ,k'arfin imani da hak'uri yashiga zuciyarsa ,a fili ya furta "Alhamdulillah ,y'ata ina tayaki murna da samun rahamar ubangiji ,Allah yagama yimiki komai tunda yayimiki kyakkyawar cikawa ,muna rok'on ubangiji yabamu irin taki muma " yasa hannu ya shafi fuskarta idanunta suka rufe ,sannan yaja mayafi ya lullub'eta gabad'aya.

Ya kalli Mamma da mummy da suketa rafsa wani irin kuka da d'ora hannu aka ,ya girgiza kai yace "Dan Allah Aisha kuyi shiru ...tace kar ayi mata kuka ...nasan zubar hawaye dolene amma  kudena wannan ihun" Baba ya nufi Hamma sageer ya d'agoshi ya tallabo fuskarsa yana kallonsa ,sai yaga Hamma sageer d'in ya zubawa gawar Hassana idanu yanata kallonta ,ya janye jikinsa daga jikin Baba yafara takawa a hankali har ya isa kusada gawar Hassana yasa hannu ya yaye mayafin da aka  rufeta dashi ya tsuramata idanu ,addu 'a yakeyi a zuciyarsa Allah ya d'auki ransa shima ya mutu a wajen ,sai yakife kansa a k'irjin Hassana hawaye na ambaliya ,da raunanniyar murya yace "na rasa mahaifina alokacin da nake buk'atarsa ,kema narasaki alokacin da nafi kowa sonki da buk'atarki ,me zan zauna nayi a duniyar da babu ke acikinta ,Allah ka d'auki raina nabi masoyiyata ....wayyo Allah zuciya ta " wani irin tari ya sark'eshi kawai sai ya k'arasa kifewa akan k'irjinta ya sume.

Ita kam Hussaina ma batasan inda kanta yake ba awannan lokacin ,daga ita har Hamma sulaiman a daskare kawai suke ,saida Baba yabashi umarnin yataso sannan ya iya ajiye Hussaina ya jinginata da bango ya mik'e ,shi da Baba suka had'u suka d'auke Hamma sageer daga kan Hassana suka kwantar dashi a gadon Hussaina ,Baba da kansa ya kirawo doctor Wanda yake k'ok'arin shigar da Hassana tiyata ,shi kansa doctor yaji mutuwar sosai saida ya razana ,yace yajima baiji mutuwar da ta dakeshi kamar wannan ba ,shine yabawa Hamma sageer taimakon gaggawa ya farfad'o ,babu kuma yadda ba'ayi dashi ya zauna a asibitin acigaba da kula da lafiyarsu shida Hussaina ba amma yak'i ,banda hawaye babu abinda yakeyi ,yana kusada gawar Hassana yakasa matsawa daga inda take.

         Baba ne yaja Hamma sulaiman gefe yace "ina wayarka ...!?Hamma sulaiman da ya zama baya gane fari balle bak'i saboda tsananin tashin hankali yasaka hannunsa a aljihu yana lalubar wayar ,yana d'akkowa ya mik'awa Baba ,Baba bai karb'a ba yace " lalubomin lambar Aminullahi "sai Hamma sulaiman yace " bazan iya ganin komai ba a wayar Baba ,idanuna dusu dusu suke gani "Baba ya girgiza kansa yana salati ,yasan shak'uwar Hassana da sulaiman me girma ce, tilas ya gigice da ganin mutuwarta.

HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now