page39to40&41to42

683 42 0
                                    

[2/3, 2:13 PM] Hassana D'an Larabawa🥰: _________________________________

*TYPING*📲

💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣

*TAREDA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page3⃣9⃣to4⃣0⃣*







*TUNASARWA*👇

*MANZON ALLAH (S A W)YACE "DUK WANDA YABAR JUMA'A SAU UKU BAIJE MASALLACI BA ,KAWAI DOMIN KASALA ,KO KUMA DOMIN SASSAUCI DA AL'AMARINTA (JUMA'AR)FACE ALLAH YA KIFE ZUCIYARSA,(SAI DAI INDA WANI DALILI)" DUK WANDA YABAR YIN SALLAR LA'ASAR AYYUKANSA SUN B'ACI*"





*AIKI ME FALALA*👇


*MANZON ALLAH (S A W)YACE"DUK WANDA YAYI SALLAR ASUBA CIKIN JAMA'A ,SANNAN YA ZAUNA YANATA AMBATON ALLAH HAR FITOWAR RANA,SANNAN YAYI RAKA'A BIYU ZAI SAMI LADA KAMAR HAJJI DA UMRA CIKAKKU*

WATTPAD:hassana3329

® _PEN : WRITERS  ASSOCIATION_
_________________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~

https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/







Wata d'aya bayan haka sukayi candy a Makaranta ,ranar duk k'awayensu na murna amma su kuka suka dinga yi ,ganin ranar rabuwa nata matsowa agaresu ,duk sun rame saboda k'ulafuci .


Ya Abdurrahman tun yanawa Hussaina dariya har yadawo lallashinta saboda yaga tad'aga hankalinta da yawa ,indai yazo haka zata sakashi a gaba da kukanta ,takance masa "ya Abdurrahman ni duk naji banson yin auren ma ...badan komai ba sai banason narabu da rabin raina ,gashi wannan Abokin naka zai k'ara nisantani da ita" sai takuma fashewa da kuka .

          Abdurrahman fuskarsa da jimami yace "aure bafa rabuwane na din din dinba, yawan kukannan da kikeyi yana bani mamaki kamar zaki auri Wanda bakyaso tawan....!? Idan baki daina ba zan had'aki da mummy wallahi ,kinga yadda kika rame kuwa ...!?duk k'ashi yafito miki a wuya ...haka kikeso akaimin ke k'ashi da rai babu wata kyakkyawar tsoka da hannu zai tab'a yaji dad'i......!? Da hawaye a fuskarta amma saida ta harareshi saboda jin abinda yace ,ya tuntsire da dariya yana kai hannu wuyanta yad'an tab'a k'ashin wuyan yace " da gaske fa ...Dan Allah dubi k'ashi b'aro b'aro ....ki kwantarda hankalinki kina tare da Hassanarki babu me rabaku ....yawan kuka da damuwar da kikeyi shine yake sakawa itama tashiga damuwar fa ...wallahi garake kinfita cab'awa ma ...zaki zauna gari d'aya da danginki da iyayenki ...gani yayanki zan zamemiki miji agareki ,zan nunamiki soyayyar da zatasa ki manta da Hassanar ma "ya k'arasa yanai mata gwalo ,aikuwa takuma fasa kuka tana diddira k'afafu cikin kuka tace" wallahi babu wani dad'i ko soyayya da zatasa na manta da ita ....ya Abdurrahman kana raina yawan soyayyar da nake matako ....!?ban san ya ranar rabuwarmu zata kasance ba ...inasonta wallahi ,na rantse ya Abdurrahman ina tsananin k'aunarta "ganin kukan da takeyi yasa yakamo kafad'unta ya rik'e gam, cikin sanyin murya yace " tawan "ta kalleshi fuska duk tafara kumbura saboda tsananin kuka ,ya lumshe ido yabud'e yace " wasa nake miki ,ai nasan soyayyata tayi kad'an ta mantar dake rabin ranki....kiyi hak'uri kinji ,nasan kina tsananin sonta ,nima kuma zanci gaba da tayaki sonta ....."ta d'an fad'a gefen kafad'arsa ta jingina da k'irjinsa tana ajiyar zuciya ,baiyi niyyar rungumeta ba amma haka yasa hannunsa ya rungumeta a jikinsa yana jijjigata ,wata irin soyayya na ratsa jikinsa da tausayinta ,a haka har bacci ya kwasheta a jikinsa saboda bata samun bacci da daddare sai yawan kuka .

Saida baccin yayi nisa sannan ya zameta a jikinsa ya kwantar da ita kan kujerar d'akin nasu,ya gyara mata kwanciyar harda samata filon kujera a k'irjinta ,yagoge mata busassun hawayen fuskarta ,tausayinta yakeji sosai a ransa ,mik'ewa yayi yafito daga d'akin ya tarar da Umma a ktcheen tana girki ,ga Hassana a zaune kan tabarma a tsakar gida tana yanka salat ,Usman kuma a gefenta yanata had'a mata salat d'in yana bata tana yankawa .

HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now