page 15to16

802 53 0
                                    

*TYPING*📲


💔👭 *HASSANA* 👭💔

                  *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣




*TARE DA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page 1⃣5⃣to 1⃣6⃣*


WATTPAD:hassana3329



*TUNASARWA*👇

*MANZON ALLAH (S A W )YACE "NA HANEKU DA YIN HASSADA ,SABODA HASSADA TANA CINYE AYYUKAN K'WARAI ,KAMAR YADDA WUTA KE CIN ICE KO KUMA CIYAWA*"



*AIKI ME FALALA*👇

*MANZON ALLAH (S A W ) YACE "DUK WANDA YAYI MIN SALATI SAU D'AYA ,ALLAH ZAIYI MASA GUDA GOMA ,KUMA ZA'A GOGE MASA KURA KURAI GOMA ,KUMA ZA'A D'AGA DARAJARSA SAI GOMA,A WATA RUWAYAR MA ZA'A RUBUTA MASA LADA GOMA*"




Ganin irin kallon da y'an biyun ke musu yasa mamma bud'e baki tana murmushi tace "mamakin ganin mu ne yasa kuka kasa magana sai kallo da ido ....!?habawa ai sai kunya takama Hassana ...ta janye idanunta da fad'in" mamma sannunku da zuwa ....Aunty Nafeesa barka da zuwa Ku shigo mana ...."tsam ta tsame hannunta daga kumfar wanke wanken ta mik'e domin yi musu iso d'akin Umma .

        Ganin zasu shige yasa Hussaina ta gaishesu ...suka amsa mamma nacewa "sannu da aiki Hussaina" sannan sukabi Hassana da ta tsaya tayi sallama k'ofar d'akin Umma da fad'in "Umma munyi bak'i nefa" Umma tace "bak'i kuma....? Toh sannunsu da zuwa ....kai usmanu d'auki kwanan zogalen nan ka kai min kitchen ka Adana ....Hassana kice su shigo "inji Umma da ke k'ok'arin gyara zamanta .

        Hassana ta juya tana cewa " Ku shigo mamma "mamma tace " to madallah "sannan suka shiga d'akin Umma da sallamar su .....Umma ta mik'e tanayi musu maraba lale ,sosai Umma ta tarbesu duk da batasan mamma ba amma tasan Aunty Nafeesa ....kuma ganin Nafeesa tare da mamma ta tabbatar akwai wata alak'a tsakaninsu ko Dan kamar da taga sunayi .

      Bayan sun zauna suka gaisa da Umma ,Hassana ma ta gaishesu tare da zuwa takawo musu ruwa .....basajin k'ishirwa amma Dan kar aga kamar sun raina sai suka sha ruwan tare da godiya .....Hassana tashi tayi tafita domin cigaba da Aikin da sukeyi ....Usman kuma yazo ya gaidasu mamma yanata yimata murmushi alamar ya ganesu ....mamma harda kawo masa tsarabar chocolate da biscuit masu dad'i ....usaman yak'i karb'a yana kallon Umma yana sunkuyar da kai yace" ah ah kibarshi "mamma tace " haba yaro me wayo ka karb'a mana ainima mamanka ce ko...!?saida Umma tasa baki sannan Usman ya karb'a yace "angode Allah yasaka da alkairi"

Bayan Usman ya fita daga d'akin ne Aunty Nafeesa ta gyara zamanta tadubi Umma tace "Umma wannan mahaifiyata ce....ta haifemu mu biyu nida k'anina sageer ...to maganar gaskiya akwai wata matsala da ta shiga tsakaninta da sageer d'in wadda tazame mata k'alubale ...kullum cikin Neman hanyar gyara lamarin muke Allah baisa andace ba ....sai yanzu ne muke ganin kamar maganin matsalar tazo .....Umma bawani abune maganin matsalar ba face Hassana .....itace muke ganin zata taimaka mana ta shawo mana kan matsalar nan .....shine mukazo gareki Umma Dan Neman taimakonki akan mamma zata tattauna wasu maganganu da Hassana d'in ....ta hakane kawai muke ganin za'a samu maslaha insha Allah "

        Umma tacika da mamaki a zuciyarta sai dai bata bayyana a fuskarta ba ....mamakinta bai wuce a ina sukayiwa Hassana sanin da har suke mata kallon maganin matsalarsu ....!? Ita kanta Naffesar bawani sabo sukayi da itaba dalilin su ba masu cusa kai bane ....balle mahaifiyarta da yau kad'ai ta tab'a ganin kalarta ma .....Umma tanada tabbacin yaranta basuda shige shige da cusa Kansu a gun mutane ....to amma ya akayi aka haihu a ragaya ..... !?

HASSANA DA HUSSAINA Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang