page 27to28&29to30

727 41 2
                                    

[1/23, 1:44 PM] Hassana D'an Larabawa🥰: _________________________________

*TYPING*📲

💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣

*TAREDA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page2⃣7⃣to2⃣8⃣*

WATTPAD:hassana3329

® _PEN : WRITERS  ASSOCIATION_
_________________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~

https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/groups




*TUNASARWA*👇

*MANZON ALLAH (S A W)YACE "BABU WANI MUTUM DA ZAICE DA D'AN UWANSA YA KAI KAFIRI,FACE D'AYANSU YA CANCANCI KALMAR" IDAN YA KASANCE YADDA YA FAD'A D'IN GASKIYANE TO SHIKENAN,IDAN BA HAKABA NE KUWA ,TO KALMAR ZATA KOMA KANSA*



*AIKI ME FALALA*👇

*MANZON ALLAH (S A W)YACE "DUK WANDA YA KARANTA AYATUL KURSIYYU BAYAN KOWACE SALLAR FARILLA ,BABU ABINDA ZAI HANASHI SHIGA ALJANNA ,SAI DAI MUTUWA*




D'AN DABA KUMA..!?tawan yaushe sageer ya zama d'an daba kike ambatarsa da wannan KALMAR ....!?

Ta cono baki gaba tana hararan hoton hannun Hassana tace" ya Abdurrahman shaye shaye fa yake ...kuma yana raina mahaifiyarshi kaga ai yazama d'an daba kenan" ya d'an lumshe idanu ya waiwayo yadubi Hassana yace "rabin ranmu a ina kukasan sageer ....menene alak'arku dashi ...!?Hassana da tayi tagumi tad'anyi ajiyar zuciya ta kalli sisinta tayi murmushi ..sai kuma ta kawar da kanta zuwa ga Abdurrahman tafara bashi labarin lokacin da suka San sageer har zuwa ,amma bata fad'amasa dalilin da yasaka sageer shiga mummunan hali ba " kawai sun tsinci Abdurrahman na hawaye da idanunsa ne alokacin da yake furta cewar "wannan halayyar da sageer ya b'ullo da ita tun bayan rasuwar mahaifinsa itace silar rabuwata dashi ,sageer Amini nane tun muna secondary har zuwa jami'a ,wannan hoton da kika gani mu hud'u a jiki sageer ne da ni ,sai kuma abokanmu guda biyu faruk da muktar ,ko a Makaranta mu hud'u ne group d'inmu mun shak'u da juna sosai ...amma nafi shak'uwa da sageer saboda mutuncinsa da karamcinsa ,ga hankali da cikakkiyar nutsuwa da kamala ,bashida yawan magana ko kwaramniya da shashanci irin na mazan zamani wad'anda da sunga Allah yayi musu kyakkyawar sura da kud'i da k'uruciya sukeyi ,wallahi bazan iya fad'amuku yawan y'ammatan da suke kawowa sageer hari a lokacin ba amma baya kulasu karatune kawai a gabansa ,faruk shine yafita zakka a cikinmu saboda shaye shayen da yakeyi ,muna iyakar k'ok'arinmu wajen ganin ya daina ,musamman sageer da kullum cikin yimasa nasiha da fad'a yakeyi ,kwatsam bayan rasuwar mahaifin sageer sai na tsinci sageer yabi layin da faruk yakebi ,ma'ana shima yafara shaye shaye ,randa na tsinci sageer a d'akin faruk a buge cikin maye nayi bak'inciki da takaici mai yawa ....ko da sageer yadawo hayyacinsa a maimakon nayi masa nasiha sai na haushi da bala'i ina kuka, na gayamasa maganganu marasa dad'i da d'aci ,nace masa bani bashi tunda yazama mutumin banza ,nayi tafiya ta na barshi anan ,daga ranar bansake ganin sageer ba ...daga baya nayi tunanin abinda nayi bashine dai dai ba ,kamata yayi nazauna dashi naji damuwarsa inyaso nabashi shawarwari da nasiha ,nasan zai d'auka insha Allah,amma nayi sintirin zuwa gidansu sageer bana samunsa hatta mahaifiyarsa bana samunta ...haka nan nake zuwa gun faruk Dan naji labarin inda sageer yake, amma yace shima bai saniba ,mahaifiyarsa da yayarsa sunzo sun d'aukeshi "a yanzu babu abinda nakeso irin naga sageer ko domin nasan dalilin fad'awar sa wannan mugun hali da yafi tsana ,amma kuma yafad'a ciki".


       Hassana ta nisa bayan Abdurrahman yagama bayaninsa ,tace" ya Abdurrahman kanason kasan dalilin fad'awar Hamma sageer cikin wannan halin ko ....?ya d'aga kai yana cewa "tabbas inason sani" sai Hussaina ta katsesu da cewa "ya Abdurrahman please kaci abincinka kar ya huce ...kubar maganar mutumin nan haka " ya juyo yana kallonta da murmushi a fuskarsa yace"ki d'an yimin uzuri tawan, inason jin labarin sageer ne ,indai abinci ne zanci har ...."kafin ya kamala maganarsa ta tashi fuuu tayi waje tana kumbura fuska .

HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now