page 57 to 58

726 48 4
                                    

_________________________________

*TYPING*📲

💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣

*TAREDA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page5⃣7⃣to5⃣8⃣*

WATTPAD:hassana3329

® _PEN : WRITERS  ASSOCIATION_
_________________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~

https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/






*TUNASARWA*👇

WUTA

*KAFIRAI ZASU SHIGETA TARE DA WASU MASU LAIFI CIKIN MUMINAI ,ACIKIN MUTUM DUBU MUTUM 999 NE ZASU SHIGA,TANADA K'OFOFI BAKWAI ,TAFI WUTAR DUNIYA SAU SABA'IN KAFIRAI ZASU K'ARA GIRMA ACIKINTA DOMIN SU D'AND'ANI AZABA ,HAK'ORANSU KUMA KAMAR DUTSEN UHUDU ,ZA'A KAURARA FATARSU AKUMA DINGA CANJA TA DOMIN SU D'AND'ANI AZABA.ABIN SHANSU RUWAN ZAFINE MAI ZAFI YANA TSINKA HANJI,ABINCINSU KUMA ZAKKUM NE DA GISLIN DA MUGUNYA,WANDA YAFISU SAUK'I KUMA SHINE WANDA ZA'A SA GARWASHI A K'ASAN DIGADIGANSA K'WAK'WALWARSA TA DINGA TAFASA,FATARSA TA NARKE TA RUB'E TA SALUB'E ,RAMINTA ZURFI NE DASHI ,DA ZA'A JEFA MUTUM CIKI ZAI KAI SHEKARA SABA'IN BAI KAIBA ,KAFIRAI DA DUWATSU SUNE MAKAMASHINTA ,ISKARTA MAI ZAFICE INUWARTA MA ME ZAFICE ,,TUFAFIN CIKINTA MA NA WUTA NE ,TANA CIN KOMAI BATA BARIN KOMAI ,TANA HAD'IYAR FUSHI TANA K'ARAJI TANA CIMMA K'ASUSUWA DA ZUKATA*

ALLAH UBANGIJI KA KAREMU KA TSAREMU DAGA AZABAR WUTA IDAN MUN KOMA GAREKA YA ALLAH 👆😭😭






*AIKI ME FALALA*👇

*MANZON ALLAH (S A W) YACE "NIDA WANDA YAKE D'AUKAR D'AWAINIYAR MARAYA KAMAR HAKA MUKE ,YA HAD'A YATSUNSA GUDA BIYU MANUNIYA DA KUMA D'AN TSAKIYA (WATO YA HAD'ASU GURI GUDA*




*Innalillahi wa"'inna ilaihirraji'un ,feedyn bash inai miki ta'aziyya abisa rasuwar kakar ki ,Allah ya jik'anta yayi mata Rahama*🙏🙏🙏






*BARKANMU DA JUMA'A SISTERS ,ALLAH YABAMU ALBARKACIN WANNAN RANA ME ALBARKA*🥰🥰🥰









***D'agowa yayi yana duban inda yaji sallama ,sai yaga wata mace tsaye akansu fuskarta da fara'a tana dubansu hannunta d'auke da robar ruwa ta swan water ,murmushi takuma yimasa sannan tace" sannu ,hala batada lafiya ne .....!?ya kalli Hussaina tanata faman lumshe idanu sannan yadubi matar yace "tun tahowarmu amai yake damunta ...so sai yanzun tasamu ya zubo ..." Ta D'an tsuguna tana mik'a masa ruwan hannunta tace "ayya amshi ka wanke mata bakinta tun acikin jirgi nalura cewa kamar batajin dad'i... Ina ganin abinda yasata aman ko laulayi takeyi ...!?yad'an tsurawa matar idanu yana juya idanu da kai ,to aishi baima san menene laulayin da ta ambata ba ,shiyasa yace " laulayi kuma ...!?menene laulayi ....!?matar tayi dariya tace "ba matarka bace ...!?ya d'anyi shiru saboda shi har yanzun bai San awane matsayi Hussainan take ba ,da taga yayi shiru sai tace" ina nufin ko ciki ne da ita shine yasata laulayi har take amai ...!?

        Ba Hamma Sageer ba Hatta Hussaina saida maganar matar taso bata dariya musamman ganin yadda Sageer d'in yayi wuk'i wuk'i da idanu ,suna had'a idanu da Hussaina ya galla mata harara yana k'ok'arin bud'e murfin robar ruwan hannunsa ,matar ta mik'e tana cewa "toh sai anjimanku Allah yak'ara sauk'i ya raba lafiya ....duk da ban sanku ba hakanan naji kun burgeni" tana gama fad'in haka tayi gaba tana murmushi .

Da kansa ya d'auraye mata bakinta ,adai dai lokacin da motar hotel d'in ta k'araso inda suke, drivern yafito yana gaida Hamma Sageer ,sannan yafara kwasar jakunkunan su yana sawa acikin Boot d'in motar, Hamma Sageer yabud'e motar da niyyar shiga ya waiwayo yana kallon Hussaina dake durk'ushe batada niyyar tashi ,ya D'an tsuke fuska yace "malama mutafi mu barki anan ne ...!?naga bakida niyyar tashi ..." Da k'yar ta yunk'ura ta mik'e tsaye tanajin kanta na juyawa hajijiya na kwasarta ,tafara nufar motar tana tangad'i tamkar takifa ,da hanzari yayi niyyar tareta cikin wata irin murya me kama da fad'a yacemata "na rantse in kika fad'i ke kika jiyo ....ba ruwana ni .."tilas haka ya rik'e hannunta yasata cikin motar sannan shima yashiga ciki ,driver yaja motar suka tafi .


HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now