page 21to22&25to26

765 40 2
                                    

[1/16, 5:22 PM] Hassana D'an Larabawa🥰: *TYPING*📲


💔👭 *HASSANA* 👭💔

                  *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣




*TARE DA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍



*page2⃣1⃣to2⃣2⃣*




WATTPAD:hassana3329



DEDICATED TO

*HUSSAINA D'AN LARABAWA (SISINA) BAZAN CE KOMAI A KANKI BA DOMIN KIN SAN K'AUNAR BA MAI YANKEWA BACE ,ZUCIYAR HASSANAR KI KULLUM CIKE DA K'AUNARKI TAKE,INAI MIKI ADDU'AR FATAN ALKAIRI HUSSAINA TA*😍😍😍


*ALHAMDULILLAH*
*ALHAMDULILLAH*
*ALHAMDULILLAH*

*GODIYA TA TABBATA GA ALLAH(S W A ) MAD'AUKAKIN SARKI DA YA BANI LAFIYAR CIGABA DA RUBUTA MUKU WANNAN LITTAFI ,TSIRA DA AMINCI SU TABBATA GA SHUGABAN MU MASOYIN MU ANNABI MUHAMMAD (S A W ) NI HASSANA D'AN LARABAWA NA GODEWA ALLAH ,NA KUMA GODEWA IYAYE NA DA MIJINA DA YARANA DA Y'AN UWANA DA DANGINA DA K'AWAYE NA DA MAK'OTA NA DA MASOYA NA A DUK INDA SUKE ,LALLAI RUBUTU BAIWA NE WANDA BAZAKA SAN HAKABA SAI IDAN KANA RUBUTU WANI ABU YAFARU DA KAI NA FARINCIKI KO AKASIN HAKA ,ANAN ZAKA TABBATAR DA CEWA KANADA TARIN MASOYAN DA BAKASAN YAWANSU BA ,A KARO NA K'ARSHE INA K'ARA CEWA NAGODE MASOYANA*🥰🥰🥰

*TUNASARWA*👇

*MANZON ALLAH (S A W )YACE "DUKKAN WANDA KUKA YABESHI DA ALKAIRI ,TO ALJANNA TA TABBATA A GARESHI,KUMA DUK WANDA KUKA AMBACESHI DA SHARRI ,TO WUTA TA TABBATA A GARESHI,KUMA KU SHAIDUN ALLAH NE A BAYAN K'ASA*

*ALLAH MUNA ROK'ON KA KASA A YABEMU DA ALKAIRI A LOKACIN RAYUWAR MU DA BAYAN MUTUWARMU*👆



*AIKI ME FALALA*👇

*MANZON ALLAH (S A W )YACE " DUK WANDA YA LAMUNCE MIN ABIN DA KE TSAKANIN HARSHEN SA DA ABIN DA YAKE TSAKANIN FARJINSA ,TO NA LAMUNCE MASA GIDAN ALJANNA*




    Shigar ta gida da sallamarta yabawa Umma damar amsawa ,wadda tafito daga bayan gida d'auke da buta a hannunta ,Hassana tace "Umma sannu da gida " kallon ta Umma tayi tace "yauwa Hassana ,menene ya tsayar dake har Y'ar uwarki tariga ki shigowa gida yau ...!?bayan kullum tare kuke dawowa ....!?kafin Hassanar tayi magana wuf Hussaina ta d'aga labulen d'akin su ta lek'o tace " Umma kin san ta da lak'ai lak'ai nikuma kaina na ciwo shiyasa na barta a hanya nayi saurin dawowa Dan nasha magani "a b'oye Hassana ta sauke ajiyar zuciya saboda yadda sisinta ta cetota ,Dan batasan me zata gayawa Umman nasuba ,Umma tace " Ayyah ,toh kin sha maganin dai ko . .!?eh nasha Umma ...munada ragowar paracetamol daman ...!inji Hussaina da ke hararan Hassana ta gefen ido ,"toh Allah ya sawak'e yabada lafiya "cewar Umma tana janyo butar gabanta Dan gabatar da alwala .

   Daga hakan Hussaina takoma d'akin yayinda Hassana tabita ciki ,Umma tad'aga murya tana fad'in" Ku fito kuyi haramar sallah ,kun San magriba da saurin wucewa ...karku bari ta kufce muku....!

          A tsawon Daren Hussaina tak'iyiwa Hassana magana ,duk yadda Hassana taso ta saurareta tak'i yarda, ba k'aramar damuwa tashiga ba ganin fushin da sisinta takeyi da ita..... Har zuwa sanda suka hallara gabad'ayansu a falon Baba ...inda Hamma sulaiman yakawo musu sababbin wayoyin su masu azabar kyau ...sunyi murna da godiya sosai ...inda Hassana ta matsa jikin Hussaina tana nuna mata tata wayar tana cewa "sisina kinga nawa wayar ...bani naki nagani kinji "sai Hussaina tayi mata banza ta juyar da kanta gurin ya safwan tana cewa " ya safwan duk gidannan Kaine d'an birni bari nazo ka koyamin yadda zanyi amfani da wayar nan "jikin Hassana yayi sanyi hawaye yaciko idanunta ganin abinda sisinta ke mata ...cikin dabara tasaka hannu tana goge hawayen yadda baza'a kula ba ..amma ina tuni Hamma sulaiman yagani ...ji kawai sukayi Hamma sulaiman da muryar b'acin rai yace " ke Hussaina. ..."Hussaina dake dab da safwan ta zura kanta ta kafad'arsa tana ganin yadda yake sarrafa wayarta cikin k'warewa ta d'ago kanta a tsorace jin yanayin muryar Hammansu tace "na'am Hamma" yayi mata wani kallo yace "zo nan " duk gurin ya d'auke wuta ana son sanin me yafaru ...ita kuwa da batasan laifin da tayiba saita taso sumu sumu tazo ta tsuguna gaban Hamma sulaiman tace "gani Hamma"

HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now