page71to72&73to74

547 41 2
                                    

[3/7, 5:12 PM] Hassana D'an Larabawa🥰: _________________________________

*TYPING*📲

💔👭 *HASSANA* 👭💔

                *DA*

❣👭 *HUSSAINA* 👭❣

*TAREDA ALK'ALAMIN HASSANA D'AN LARABAWA*✍✍✍


*page7⃣1⃣to7⃣2⃣*

WATTPAD:hassana3329

® _PEN : WRITERS  ASSOCIATION_
_________________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~

https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/











*TUNASARWA*👇

*MANZON ALLAH (S A W ) YACE "LALLAI KAR D'AYAN KU YA CI DA HANNUN HAGUNSA ,KUMA LALLAI KAR YASHA DA HANNUN HAGUNSA,DOMIN SHAID'AN NE YAKE CI DA HAGU KUMA YA SHA DA HAGU*"








*AIKI ME FALALA*👇

*BABU WAD'ANSU MUSULMAI BIYU DA ZASU GAMU DA JUNA KUMA SU HAD'A HANNU DOMIN GAISUWA ,FACE AN GAFARTA MUSU BAKI D'AYA ,KAFIN SU RABU DA JUNA*






         ***To duka duka Kwana uku ya rage a fara bikin duk wasu shirye shirye sun kammala ,sosai su Hamma Sulaiman da Adda Nabeela suka daki k'irji sukayi komai ,basu bar Baba da Umma sunyi komai ba illah su da suka d'auki nauyin ragamar komai ,
Mijin Adda Nabeela shine yasiyi furniture's a matsayin gudummawarsa ,daga k'asar waje yayo odarsu masu tsananin kyau da tsada .

       Da yammacin ranar talata da yarage saura kwana biyu a fara shiga shagalin bikin ,Hussaina ce zaune a falon Aunty Sadiya gidan Hamma Aminu ,gyaran jiki ake mata duk anshafe mata jiki da had'in kurkur da dilka da wasu sinadarai na gyaran jiki ,zaune take akan wata kujera me b'ule b'ule ansaka garwashin wuta da turare me azabar k'amshi yana turare jikinta ,babu kaya ajikinta illa k'aton bargo da aka lullub'e mata jiki dashi ,sai fuskarta kawai da aka shafawa kurkur ce a waje, mita take tayi ita tagaji da zaman so take ta tashi gashi tanajin yunwa ,ita kuma Aunty Sadiya tak'i barinta tace tilas ta zauna ta dad'e Dan gyaran yashiga jikinta sosai ,ita Hassana tuni angama mata tana toilet tana wankan turare ,yayinda Hussaina da k'er ma aka samu ta zauna aka shafa mata ,su Zahra da Asma'u da wata k'awarsu Ruk'ayya suna zaune sai dariya sukewa Hussaina da gwalo ganin yadda taketa mita tagaji ga uwar zufa da ta had'a .

        Sallamar Ya Abdurrahman tasa Aunty Sadiya mik'ewa da hanzari ta nufi k'ofar falon ta babbake hanya ,amsa sallamarsa tayi tana kare k'ofar saboda tasan indai yashiga sai ya b'ata musu aiki musamman yadda Hussaina take wani langab'ewa ,tana D'an yak'e da sosai k'eya tace "ayya Ya Abdurrahman kaje wancan falon ka zauna nan munayin wani D'an aiki ne " ta nuna masa d'aya falon da ya kasance mallakin Hamma Aminu ,wani kallo yabita dashi me kamar harara yace "ina tawan take ...!?tafara in ina da fad'in " uhmmm uhmmm daman ,daman tana cikine ana mata gyaran jiki fa ..."kawai sai yasa hannu yad'an ture Sadiya gefe yana fad'in "dalla kauce kibani guri na wuce malama " ya kutsa kansa cikin falon ,
Tunda Hussaina taji sallamarsa daman tak'ara shagwab'e fuska tana narai narai da idanu ,yana shiga ko kallonsu zahra baiyi ba yanufi gaban Hussainar ya tsuguna ,kallonta yayi yana zaro idanu yakai hannu ya shafi kumatunta yana fad'in "ke meye wannan aka shafa miki kamar dodo ...!?ta wani langab'e kai wai taga masoyinta zatayi shagwab'a ,tace " wai dilka ne Ya Abdurrahman ,kuma nagaji sunk'i wanke min ,gashi yunwa nakeji ...."sai ta matso hawaye tana kyab'e baki ,

     Ya tsura mata idanu yaga yadda take gumi ga uban bargo an lafka mata cikin d'aure fuska ya juyo yana hararan Sadiya yace "amma dai ke anyi muguwa wallahi ,ya zaki k'unshemin mata ki jibga mata uban bargo da sunan wani gyaran jiki ,Dan zalunci kuma tanajin yunwa ki hanata abinci ....!?Sadiya tafara rantse rantse da cewa " na rantse Ya Abdul yanzu aka shafa mata ,tun d'azu ake fama da itafa tak'i zama ayi mata ,tuni aka gamawa Hassana amma ita sai matsala take bamu ,kuma nace tajira agama sai taci abincin .....!?ya d'anyi tsaki yana kauda kai yace "wannan kawai zalunci ne ahana mutum abinci ,kibani abincin kawai nabata a baki tunda cikin Ku d'ima d'ima an rasa me bata " dariya su Zahra sukayi ,ma'u nacewa "inamu ina bata abinci abaki wannan ai aikinka ne Ya Abdurrahman ......

HASSANA DA HUSSAINA Where stories live. Discover now