Ashirin Da Bakwai

1.4K 198 57
                                    

Koda Ramlah ta karasa cikin gidan da wani kyakyawan murmushin kan fuskarta. Ita dai har ga Allah indai har suna fira da Dr Aliyu Allah ya sani har kasan ranta take jin dadin abun. Gashi ya iya murmushi, tunowa da drama dinsu ta dazu yasa tayi yar guntuwar dariya, bata lura Lubnah na wajen ba saidai taji maganarta, "Toh fah, yau soyayyar har bayan an dawo gida?" Da hanzari ta juya tana kallonta sai ta zaro ido. "Ji Lubnah, wake soyayyar to?"

Lubnah na hanyar wucewa dakinta tayi yar dariya, "Nidai bance komai ba, kardai ki bari diyar bawan Allah ta gane. Wannan irin kauna da ake ma ubanta ta kusa yin yawa." Ramlah dai kallonta kawai takeyi. Ita bata musa ba sanna ita batace eh ba. "Tana ma ina?"

"Tana wajen Mama, kinsan Mama da yara. Bari inje in dan watsa ruwa kafin maghrib yayi." Daga mata kai Ramlah tayi kafin ta juya ta nufi hanyar dakin Mama. Da sallama bakinta ta shiga dakin ai kuwa kafin ta rufe baki Hafsah ta rugo ta rungumeta. "Ammi, tun dazu inata jiranki, kun gama magana da Abba?"

Murmushi Ramlah ta mata tana lura da yarda Mama take kallonsu itama da wani murmushi kwance kan fuskarta, ba sai ka tambaya ba daka gani zaka san ma'anar shi. "Mama tana nan ta cika ki da surutu ko?" Janyo Hafsah tayi jikinta suka zauna kan kujera sannan suka gaisa da Mama, dan tun safe sai yanzu suka kara haduwa.

"Aa nikau ina yar albarka zata cikani da surutu? Firar school ake ta mani tun dazu ko Hafsah?" Yar dariya irinta yara Hafsah tayi kafin ta mike tsaye, "Zo muje mu bar Mama ta huta, anjima sai azo ayi fira ko Hafsah?" Daga haka suka bar dakin, ita kuwa Mama har kasan ranta addu'a take Allah yasa wadannan mutane sune sanadiyar samuwar dawwamammen farin ciki a rayuwar Ramlah.

Saida sukaje daki tukun Ramlah ta lura jakar kayanta har an kawota, "Aunty Lubnah ce ta kawo maki jakar ki nan?" Yar dariya tayi irinta yara idan sunyi abunda basu kyauta ba, "Dakinta ta kaita, wai can wajenta zan rika kwana. Ni kuma na fara kuka nace dole saidai wajenki, shine fa ta maido man wai munyi fada kuma ta kaini wajen Mama." Dariya Ramlah ta fara, "Anjima zamuje a bata hakuri ko? Ko kinaso ta ki baki toy din ne?" Girgiza mata kai tayi da hanzari. Daga haka suka cigaba da labari ita dai Ramlah babu abunda takeyi sai dariya, dan kusan rabin labarin duk wasan yara ne. Sai dunyi fira sunyi fira sai ta tuno labarin da Dr ya bata, ko ya sukayi rayuwa? Tanaso taji sauran labarin amma kuma batasan jin abunda ya faru, kuma daga gani ko dan ta rikice Dr yana iya cewa zai fadi mata.

Tare sukayi sallah, ita Ramlah har mamakin wayon Hafsah take dukda cewar Hanan ma kusan haka take kamar ba karamar yarinya ba. Sai can bayan sallar isha'i suka sauka kasa don cin abincin tare, dan kuwa wayar Ramlah dama tana hannun Hafsah babu abunda take bugawa sai game.

Dukansu zama sukayi kan dining din aka zuba abinci, dakyar Ramlah ta samu ta karbi wayarta tukunna Hafsah ta dan ci abinci, karshe dai sai cookies ta dauko mata da yar madara, wanda hakan da tayi sai ya tuna mata bataga Rayyan ba tun rabuwar da sukayi a shago. Lubnah na shigowa kitchen din ta fara magana, "Lubnah mutuminki bai shigo cin abinci ba, ko zaki kai mashi?"

Kasake Lubnah tayi tana kallonta, tana san tayi hakan amma kuma batasan ta ina zata fara ba. A hankali ta fara girgiza kai alamar bazatayi ba. "Aa, Ramlah. Kila ya koshi ne ko? Kawai sai naje nace mashi naga baka ci abinci ba gashi na kawo maka? Kema ai kinsan bai yiwuwa ko?" Yar dariya Ramlah tayi tana kai mata dukan wasa, "Wai ke duk lokacin da ake san a gyara abu lokacin ne bai maki ko? Anshi, na gama hada maki tray din kai mishi kawai zakiyi. Ki dan tsaya kuyi labari..." Zata kara wata gardamar Ramlah ta aje mata tray din saman hannu tana jan hannun Hafsah. "Hafsah kima Aunty Lubnah saida safe."

"Saida safe Aunty Lubnah, karki manta alkawarina." Guiwa sake Lubnah tama Hafsah murmushi, "Bazan manta ba Hafsah, kiyi bacci ki aje game dinnan kinji?" Daga haka suka fita kitchen din tana mata dariyar mugunta, "To amaryar gobe, a dai dawo da wuri dan Allah, kar inji kar in gani." Lubnah bataji ta kanta in baccin dariyar da tayi a hankali, dan ita ji take kamar kar takai amma tasan Ramlah zataji haushi kuma ko ba komai wannan ma wani hanya ne da zaisa su kara fahimtar juna. A hankali jiki a sabule ta fita daga falon ta nufi hanyar part dinshi gabanta na faduwa kadan kadan.

MIJINA NE! ✅ Where stories live. Discover now