CHAPTER 79

2.4K 180 18
                                    

RECAP

Kwalbar ta raruma ta kwalawa ma wani sannan ta Mike ta fara bin gini aiko ta taka kwalba. Toshe bakin ta tayi tana fita aka kawo wuta hakan yasa suka bita a guje ashe sabi nigga ta kwalawa kwalbar.

Gudu suka dinga yi kamin ta samu ta labe a lungu sai haki take taji an dafa kadar ta juyowa tayi suna hada ido ta zaro ido tare da kwala ihu...

CONTINUATION

Ba kowa bane illa sabi nigga, aiko ya wanka Mata wani jahilin Mari Wanda ya sata faduwa ba tare da bata lokaci ba.
Dariya ya sheke dashi harda rike ciki, hakan ya bata daman rarumar dutse ta tashi a hankali sannan ta kwala masa.
Ihu ya saka yayi da ta fita a guje tana mai tallafo cikinta Wanda ke Mata zafi a halin yanzu.
Sauran yan daban ne sukayi saurin karasawa wajen sabi'u sakamakon ihun sa da sukaji. Tambayan sa suka fara yi lafiya ? Ya nuna musu hanyan da minal tabi. Biyu daga cikin su ne suka bi hanyar yayinda lado ya tsaya, ya tallafa masa ya tashi sannan ya fara kokarin kaishi gida.

Minal gudu ta sharara har sanda kafar ta suka daina gudu kamin ta Sami zauren wani gida ta shiga. Itacen girki ta gani a jibge gefe guda dan haka taje ta jingina a jiki babu bata lokaci tayi bacci dukda ko a jikinta  tanajin akwai abinda ya dace tayi Wanda batayi ba.

🌹🍀

Yazeed bai bude idanun sa ba sai wajajen karfe Goma na dare. Akan fuskar ayush suka fada ta sakar masa wani murmushin munafurci tare da fadin brother sannu da tashuwa. Kallon ta yayi da alamar tambaya yace brother? Tace eh karka damu dama likita yace min zaka iya manta wasu abubuwa so karka damu, San baka dukkanin information da kake bukata. Jinjina kai yayi alamun toh yana kare Mata kallo Dan shi bai ma yarda da ita ba yace wacece ke? Murmushi tayi tare da zama a bakin gadon sa ta riko hannun sa. Dan janyewa yayi tace karka damu ni muharramar ka ce,ni kanwarka ce, your baby sister ka tuna?  sakan jiki kadan yayi yace toh me yasa aka kawo ni nan? Tace saboda tun sanda mahaifin mu ya rasu kake cikin damuwa hakan yasa kake samun wani ciwon kai me tsanani Wanda yakan sumar dakai wani lokaci ko ya sabbaba maka manta wani Abu toh wannan karan da alamu alakarka da mutane ka manta.

Jinjina kai yayi domin maganan ta kama kwakwalwar sa. Yace munada mahaifiya tace eh tana gida yanzu kaga hotanta. Ta fadi hakan tana mai nuna masa wallpaper wayanta. Hoton su ne su hudu, shi da ita da mummy da umma hani. Yace toh ai Mata biyu ne wajen waccece ita? Tace me kwalliyar nanne mana. Wancan kuma umma hani ce nanny din mu. Ajiyan zuciya ya sauke yace bani ruwa insha, Darius tayi kamar shasha tace au na mance na tsaya ina maka surutu.  Murmushi kawai yayi tare da karbar ruwan yasha.

Nan dai taci gaba da masa bayanan karya shi kuwa Allah sarki bai sani ba sai shiga yake tare da rike komai da take fada masa.

🌹🍀

Gidan mahaukata sukasa aka kai mom bayan an haukatar da ita. Mai kawo abin ci ne tazo tana wulla musu hara ta iso dakin mom Wanda yake na karshe. Tana kallon mom taji kamar ta Santa kuma lokaci daya taji mahaukaciyar ta kwanta Mata a ranta. Wulla Mata nata abin cin tayi mom taso ta dauka ta kyalkyale da dariya kamin kuma tace na gode.

Fara co tayi tana yamutsa fuska da ka ganota kasan bata Saba shan wahala ba. Tsayawa kallonta tayi kawai sai taji hankalinta ya kwanta da mahaukaciyar. Bude dakin tayi ta shiga sannan ta rufe, a take mom ta fara ja da baya tana fadin karki matso kusa dani! karki matso kusa dani! Matar tace kwantar da hankalin ki ba abin da zan miki.

Zama tayi a gefenta kawai sai mom ta fashe da kuka. Matar me suna senior hauwa tace me aka miki kike kuka? Mom tace ɗa na, zasu cutar min dashi! Senior hauwa tace ina yake kuma yaya sunan shi? Shiruuuu mom tayi kamin tace nima ban sani ba, na manta sannan ta sake fashewa da kuka.

Rarrashin ta senior hauwa tayi haka sukayi hirar su dukda cewa wani lokacin mom din takan Mata hauka amma dukda haka tana zargin wani Abu tana ganin haukan mom din ba haka kawai bane.

KURUCIYAR MINALWhere stories live. Discover now