part 18

1K 47 6
                                    

_*👨🏻‍🎤DAN ISKAN NAMIJI👨🏻‍🎤*_

               _*NA*_

_*FAREEDA ABDULLAHI*_
     
       _*(Feedyn Bash)*_

_*BOOK  2*_

_*Faceebook Fareeda Abdullahi Ibrahim*_

_*Whattpad @FeedynBash*_

_*Instragtam Feedyn Bash*_

_*Snapchat Feedyn Bash6660*_

_*E-mail  faridaabdullahiibrahim6660@gmail.com*_

*_🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION_*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation



                      *85-90*


Cikin tashin hankali suka mike tsaye suna kallonsa gaba dayansu a firgice suke, "lallai Alhaji ni zaka yaudara? ni zaka rainawa hankali? Alhaji ni zaku munafunta ni zaku yaudara? ke kuma wallahi sai kin dandana shi ga gonata da ki kai, sai kun dan dana cin amanata da ku kai gaba dayanku."

Ya fice ya bar su a dakin jikin Alhaji Ghali yai sanyi shi fa ya gaji da wannan masifar ya gaji da wannan danyen aikin da suke aikatawa, wannan wace kalar rayuwace ya tsunduma kansa a ciki dan yanzu dubararsa har ta fara fitar da wasu tsutsotsi ya rasa wa zai gayawa.

Dole ya ajiye wannan dabi'ar ya kula da matarsa ya zame masa dole idan ya daka ta Baby Chakwai wallahi ba zai bar shi ya huta ba, gwara ya yiwa tufkar hanci kamata yai ya zaunar aiko ta saki wani ihu sai da ya razana.

"Lafiya Nauwara me ya sameki kike wannan ihun?" "cikina nai ya motsa" ta fada da kyar saboda yadda duburarta ke tsirinta, cikin murmushi ya shafa cikin "gaskiya munyi sake kin ga cikin nan naki ya kai kusan wata shida fa, ya kamata jibi Monday na kai ki asibiti daga nan sai na kai ki gida ki wuni ko?"

Wani farin ciki taji ta a ciki wanda tun da Allah ya halicceta ma bata taba kasancewa a cikinsa ba, dama zata kara fita daga wannan gidan? dama zata kara ganin Innarta da Malam da kawarta Maimuna a duniya? kuka tasa na farin ciki ta rungumeshi "nagode nagode Allah ya biyaka ya kara bamu zaman lafiya, Allah ya kara karkato mun da hankalinka gaba daya ka dena duk wasu abun da ya sabawa Allah."

Ya tausaya mata har hawaye yai cikin jin kunya da nauyi wanda tun da Allah ya halicce shi bai taba jin kwatankwacin wannan kunyar ba, ya rumgumeta "insha Allah na miki alkawari daga yau daga yanzu na bar wannan mummunar dabi'ar tawa bari na har abada, ina rokon Allah ya gafarta mun zunuban dana dade ina aikawata."

Rumgume shi tai cikin farin ciki suna ta murmushi haka suka kwana cikin farin ciki, washe gari lahadi da wuri yake dawowa dama karfe hudu amma ya ce sha biyu zai dawo kawai zai wani aiki nai kar ta damu cikin matukar kewar juna suka rabu ya fito ya tunkari dakin su zai dau wasu takardu.

Baby Chakwai cikin bakin ciki da bacin rai ya kwana, tashin sa kenan yaiwa abokan iskancin sa waya su kawo masa maganin da zai sha yai awa biyar cir akan namiji, wanda sai ya kusa mutuwa idan ya hau shi saboda yai alkawarin sai ya hukuntata, "sannan ina so ku kawon maganin da zan zubawa Alhaji a abun sha wanda ba mai ganewa na kashe shi kowa ya huta."

Daidai lokacin da Alhaji zai shi ga dakin yaji ana zancen kashe shi gabansa na faduwa ya juya ya fita, dakin da bai shi ga ba ke nan, to dole sai ya san abun yi dole sai ya dau kwakwkwaran mataki, gaskiya Baby Chakwai ya bashi mamaki fiye sa tunaninsa, da kyar yanke tukin da kyar yaje kasuwar hankalinsa na kan Nauwara haka kawai yaji gabansa na faduwa.

DAN ISKAN NAMIJIWhere stories live. Discover now