part 19

954 48 3
                                    

*DAN ISKAN NAMIJI👨🏻‍🎤*_

               _*NA*_

_*FAREEDA ABDULLAHI*_
     
       _*(Feedyn Bash)*_

_*BOOK  2*_

_*Faceebook Fareeda Abdullahi Ibrahim*_

_*Whattpad @FeedynBash*_

_*Instragtam Feedyn Bash*_

_*Snapchat Feedyn Bash6660*_

_*E-mail  faridaabdullahiibrahim6660@gmail.com*_

*_🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION_*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*Dedicated to my brothers: Kamalu Abdullahi ibrahim, and Safiyanu Abdullahi Ibrahim, and auta Al'ameen.*

*Second to the last page*


                     *90-95*

Nan da nan Nurse din da suka taho da gawar su kai kansa amma ina numfashi ya gagareshi fita gaba daya ya fita hayyacinsa, kowa haushi ya ke ba shi to duk wannan na meye abun da ya ke bukata nai kuma ya samu, suka dauke shi sai asibiti saboda zuciyarsa ce tai mugun bugawa.

A ambulance din suka juya da shi ba wanda yabi bayansa saboda bacin rai kowa kuka ya ke su Mama da Umma nai da Momy su kai mata wanka, su nayi suna kuka saboda yadda take ta zubar da jini suka hadata duk da yamma tayi amma haka akai mata sallah aka kaita saboda jinin.

Masha Allah ta samu jama'a tayi mutane fiye da tunanin mutum sai sannan Umma ta kira kanwarta ta sanar mata halin da ake ciki na rasuwar Nafeesat, ihu ta saka ta saki wayar kasa saboda tashin hankali "Maryam! Maryam!"da gudu ta taho cikin tashin hankali "lafiya Anty?"

Ta fashe da kuka "Maryam Allah yayi ikonsa duk abun da Allah yai, bawa ba zai wucewa kaddararsa ba bata baya wuce lokacinsa" cikin kuka ta ce "Anty menene?" girgiza kai ta ke "sai dai miyi hakuri Maryam Allah ya karbi ran Nafeesat! sai wancen dan iskan ya zuba ruwa a kasa ya sha zabi ya rage gareki yanzu ko uba ko da?dan kin san dole a nemi ki maye gurbin yar uwarki, amma zanfiso ki mana alfarmar auren uban ko dan Arfan ya gane kurensa."

Wata kara ta saka ta zube a wajen take jini ya fara bin ta cikin tashin hankali Anty tai kan ta da sauri ta kira mijinta tana kuka ta gaya masa, da sauri ya dakko shatar taxi suka tafi asibiti suna zuwa aka kai ta dakin yan bari saboda bari za tai wata biyar.

Haka ta kira Umma ta sanar mata tai mata addu'a kuma tai mata fatan alkhairi Allah ya rabata da cikin lafiya tasha wahala sannan cikin ya fadi, ba bata lokaci su kai mata wankin ciki kwananta daya tai normal suka sallameta a ranar suka wuce gidan makokin duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata halin da ta ke ciki.

Abba na gadon asibiti ya gamu da cutar paralyse saboda wannan faduwar da yai a karo na biyu Sulaiman ke jinyar sa saboda su Mama na karbar gaisuwa ba um ba um um Abba ya zama kamar gawa a asibiti, ga Arfan a kwance shi ma zuciyarsa ta buga ana tunanin fita da shi ma waje saboda halin da ya ke ciki me wuyar fassaruwa amma Daddy yaki yarda.

A yau akai sadakar uku suna zazzaune a dakin da suke Umma da Mama da Anty sai Maryam da ke kwance Mama ta gyara zama "lokaci yayi da zamu rama zalincin da Arfan yayi mana, lokaci yayi da bakin cikin da ke ranmu zai ragu."

Umma ta gyara zama "tayaya ke nan?" "yauwa ta hanyar auren mahaifinsa da Maryam za tai, kar muce zamu hana wannan auren Umman yara saboda daukar fansa" Anty ta gyara zama "ai idan kun ga ba'ai wannan auren ba to Maryam ce ta rasu amma aure ba fashi Allah nai ya halatta bamu ba."

DAN ISKAN NAMIJIWhere stories live. Discover now