Dumb out

85 11 1
                                    

💠💠💠💠💠
©®AS-2023.


*Bᴀsᴇᴅ ᴏɴ ᴀ ᴛʀᴜᴇ sᴛᴏʀʏ*


                     *♡WAZEER¸.•💥*
                   (A Tᴡɪsᴛ Oғ Fᴀᴛᴇ)


Bʏ.
   *HAWWA__B__KUMO.*
       (Rᴇᴀʟ Sᴍᴀꜱʜᴇʀ).💕
*WATTPAD:REAL-SMASHER.*
*AREWABOOKS:REALSMASHER.*
••••••••••

*It's all about:#Love one another,#Twist,#Betrayal,#Friends,#Fate,#Romance,#Hated, & #Lost..*

*MIKIYA WRITER'S ASSO..*

                               05

#Dumb out

*CALIFORNIA..*

                 Tunda suka zo ƙasar Hamood yai ciku²nsa ya samarwa Wazeer makaranta me kyau,wani private school ne a nan Hollywood Schoolhouse,dake basu da nisa daga gidansu zuwa North McCaddden Place,kullum idan zai tafi aiki zai fara biyawa ya ajiye Wazeer,sannan ya wuce ya tafi gurin aikinshi,tun safe idan Wazeer ya tafi school bai tasowa da wuri,a duk inda Hamood yake lokacin tasowarshi na yi zai dawo ya ɗaukeshi,idan ya mayar da shi gida zai siya masa abinci da komai da zai buƙata,daga nan zai koma Company'n magunguna da yake aiki,ba shi zai dawo gida ba sa can yammaci zai shigo gidan,haka zai zo ya tarar da Wazeer kamar maraya ya takure a guri ɗaya,idan ya tambayeshi mene ne sai dai ya girgiza masa kai yace "nothing" sai idan yaga damuwa sosai tare da shi,in ya matsa masa da tambaya sannan zai tambayeshi Mimi,da farko Hamood sai dai yai masa faɗa,amma da ya fahimci siye zuciyar ɗansa sai da dabara,a hankali ya fara masa magana cikin sanyi² yace "idan ka saki jikinka muka zauna a nan,then ka dage kayi karatu ka zama babba,i promise u zan kaika gurinta,ok?" A hankali Wazeer ya gyaɗa masa kai yace "ok!" Hamood ya bashi hannunsa yace "deal?" Wazeer yace "yes deal.." Ya ɗora hannunsa kan na Dad ɗinsa,Hamood yai murmushi yace "ok! Chapter close,daga yau babu tambayar Mimi,har ka gama school" a hankali yana kallon mahaifin nasa ya sake cewa "zan yi karatu Dad,idan na girma na zama Doctor,sai na dunga yiwa mutane allura" Dad yace "yessss! That's My boy,kayi karatu ka tara dukiya,ka samu suna da ɗaukaka shi ne burina,ina so ka zama babban mutum a ƙasata,ka zama wanda duniya za ta sani,duk inda ka shiga ya zama ana sunkuya maka,ana baka girma.." Wazeer yai shiru kamar yana tunani,a hankali kuma sai ya gyaɗa kanshi yace "ok Dad.." Wannan maganar ya taimaka wajen sauko da zuciyarsa,Hamood ya ji daɗi sosai da yaga ya fara sakewa,kullum baida aiki sai na jansa a jikinsa,yana zuwa school ɗinsa hankalinsa kwance,gidansu su kaɗai ne daga su sai cook ɗinsu me suna Joseph dake zuwa,shi zai gyara gidan yai musu girki,da idan yazo yana gama abunda zai yi yake tafiya,amma daga baya sai Hamood yai masa magana ya dunga zama da Wazeer kafin ya dawo saboda damuwar da yake shiga idan baya nan,dake ya samu ƙarin kuɗi sosai bai musa ba,a hankali tun Wazeer bai sakewa da shi har ganinsa yau da gobe tasa ya fara sakin jikinsa,Allah ya yi shi wani irin yaro ne da bai sakewa da mutane da wuri,har ta kai wani lokaci idan akwai abunda babu a gidan,Joseph zai ɗaukeshi su fita suna tafiya Wazeer na tambayarshi,haka kou idan yana kitchen Wazeer zaije gurinsa,ya tsaya yana ganin abunda yake,tun daga lokacin dukansu suka mayar da hankali kan abunda ya shafesu,Wazeer ya mayar da hankalinsa kan karatu sosai,duk sanda zai tadowa Hamood zancen Mimi,zai ce masa "ba yanzu zan kaika ba,ai mun yi deal sai ka zama babba,ka gama karatu" da haka ya dunga ɗauke masa hankali,a hankali lokaci ya fara tafiya daga kwanaki,satittika zuwa watanni,tunda suka tafi sam babu ruwan Hamood da zuwa gida sai dai waya,Daada tun tana masa faɗan yar da su da yayi har ta koma nasiha da lallaɓashi,amma sai dai yace mata zai zo,lokaci ne bai samu yanzu sosai,idan ƙarshen shekara yayi lokacin Eid zai zo,dake suna yin family meeting,dangi kowa zai zo daga inda yake,a haka akai first Eid-ul-fitr babu Hamood da ɗansa,da fari lokacin su Daada sun yi zaton yana gurin Hoor,sai da babbar sallah ya taho lokacin Abba yasa aje a taho da shi yaga ƴan uwansa,ɗan saƙo ya dawo ya sanar musu cewar ai Hamood yaje ya ɗauke ɗansa,wannan al'amari ya ɓatawa Abba rai,sai dai bai ƙasa a guiwa ba yaje ya sanar da Sarki Abduljalal da brothers ɗinsa,suka ce ya rabu da shi ya bashi lokaci,har Mai martaba ya bashi misali da kansa yace "nima haka nan nake fama da Mujaheed,da alama halinsu ne yazo ɗaya,ai dama ba'a ɗaya a dangi,kada kace za kayi fushi da shi,aita musu addu'ah in sha Allah komai zai yi sauƙi,komai yana da lokaci" dake duk abunda Mai martaba ya faɗawa ƴan uwanshi basa masa musu,haka Abba Waziri ya share batun,kou kiransa Hamood yayi zai ɗauka su gaisa,sai dai dai² da sau ɗaya bai taɓa nuna masa ya san Wazeer na tare da shi ba,tunda har ya iya ɓoye musu ya tafi da shi,suma ba abu ne me girma ba a wajensu su nuna basu sani ba,wani lokaci kuma yakan ce masa "Hooriyah ta tafi da Aliyu kou?" Hamood yace "Mmmm" Abba yace "tou amma shi kenan ta yanke masa zumunci da mu? Baza'a dunga kawoshi dangi ba sai ya tashi bai san kowa ba?" Hamood yace "zan yi mata magana" Abba cikin mamakin halin Hamood ya gyaɗa kanshi,wai shi Hamood zai ɓoyewa zancen,duk yanda zai bugi cikinsa bai taɓa fitowa ya sanar masa suna tare,kawai sai ya watsar da maganar,komai daɗewa ai wata rana zai dawo ya sameshi. Cikin wannan yanayin shekaru suka fara tafiya,lokacin Wazeer na da shekaru 12 wanda yai dai² da sun samu 4 yrs a ƙasar,idan kaga yanda yai girma a shekarunsa za kai zaton ya kai 15,dan a tsaye yanzu ya kusan kamo Hamood,yana ƙara girma kyaunsa da kammaninsa da Hoor suna sake bayyana,haka ma halinshi na miskilanci sai abunda ya ƙaru. Wata rana Hamood na aiki parlour,Wazeer ya samu Dad ɗin nasa,sanda ya zauna gefensa a hankali da huskey voice ɗinsa yace "Dad ina so a canja min school" Hamood dake aiki MacBook gabansa yace "shi wannan da kake yi me yayi?" Wazeer yai shiru,Hamood yace "i'm asking me ya samu wanda kake yi?" Wazeer yace "Dad ba na jin daɗinsa ne,na fi so ka mayar dani school da yake only boys,ban son mix da girls bana jin daɗinsa" Hamood bai tsaya ya fahimci damuwar da yake ciki ba yace "ok! Kaje sai na duba tukuna" daga nan Hamood bai sake tada zancen ba,in fact yama manta,ganin shiru² Dad bai ce masa komai ba shi kuma kawai ya yanke hukuncinsa ya daina zuwa,sai da aka kwana biyu aka kirashi daga school ɗinsu Wazeer,ake sanar masa bai zuwa school,kuma shi a matsayin mahaifinsa baije ya sanar yana da wani matsala ba da yake hanashi zuwa,afujajan Hamood ya sameshi,a kausashe ya kirashi "Wazeer!" Wazeer dake kwance bedroom yana kallon Korean film yai saurin pausing yace "na'am" Hamood yace "me yasa baka zuwa school?" Cikin damuwa Wazeer yace "Dad ni ba na son school ɗin,na ce ka canja min wani ka ce sai ka yi shawara,kuma baka ce komai ba,ba na jin daɗin makarantar kwata²" Hamood yace "ok! Idan na kaika wanda kake so shi kenan?" Wazeer ya gyaɗa masa kai yace "yes Dad" Hamood ya girgiza kanshi kawai ya wuce abunsa. Cikin satin ya karɓi transfer ɗin Wazeer daga Hollywood Schoolhouse zuwa International School Of Los Angeles dake Russell Ave,shima ɗin dai mix ne boys and girls,yawancin schools da suke only boys da Hamood ya duba,sai wanda ake koyar da addinin Kiristanci da yanda za ai bautar Yesu Almasihu,shi kuma duk taɓarɓarewarsa da rayuwa cikin Yahudawa,da zama ƙasar da ba tashi ba,bai gurɓata tarbiyyarshi ba,ya samu ingantacciyar rayuwa me tsafta,Abbansa bai basu ƙofar da za suyi wani abu da ya saɓawa addini ba,sai dai idan a bayan idonsa su aikata wani abu na badai² ba. Hankalinsa kwance yake tafiya school tunda Dad ɗinsa ya canja masa sabuwar makaranta,a shekarunsa yanzu babu abunda bai iya ba,har girki shi yake musu saboda zama da Chef Joseph da yayi,idan Hamood bai nan shi kaɗai yake rayuwarsa a cikin gidansu,daga school idan ya taso baida gurin zuwa sai gida,Dad ɗinsa babu abunda bai siya masa,babu abunda yake nema ya rasa,duk wani abu na jin daɗi kafin ma ya faɗa Hamood zai masa,sam bai son ganin only child ɗinsa cikin damuwa,yanzun nan zai fara tambayarshi mene ne? What do you want? A duniya maganar da Hamood bai son ji a bakinsa shi ne abunda ya shafi mahaifiyarsa Hoor,shima kuma tunda ya fara wayo ya fuskanci akwai abunda ya haɗa iyayen nasa ya bar yi masa maganarta,but deeply yana tare da tunaninta,da damuwar son ganin mahaifiyarsa yake kwana ya tashi,sai dai ta ina zai isa gareta? Shi ne abunda bai sani ba,he had a notebook and phone,amma bai kiran kowa bai da number kowa daga family'nsa,daga Dad ɗinsa sai few of his friends,sam bai harka da friends mata saboda Dad bai sake masa yai tarayya da su ba,duk wata hanya da zai bi ya lalata masa tunani akan alaƙa da mace ya yi nasara a gurin nan,rayuwa a ƙasar da ba naka ba kuma ba al'adunku ɗaya ba,sai dai Allah ya ceceka kawai,musamman ace ka buɗe ido ne ka ganka tsakiyar masu jajayen kunne,wanda addininku yasha bamban,sau da yawa friends suna gayyatarsa night party,irin wanda za'a haɗu club da ƴan mata,ayi shaye² ai rawa har a samu keɓewa kou lalata,sai dai yace musu yana da abun yi a gida,sau ɗaya bai taɓa zuwa ba,duk irin maganar da za'a faɗa masa idan an haɗu school,bai damuwa bare ya kula,ya san Dad yaji labarin ya yi wani abu zai ɓata masa rai,yana da gudun abunda zaisa ace ya yi laifi,masifar gudun abunda zaisa yai masa faɗa yake,a rayuwarsa shi wani irin murɗaɗɗen mutum ne da bambantan halaye,yana da fitinannun friends wanda basu ɗauki shaye² wani abu ba face wayewa,suna hulɗa da ƴan mata suyi abunda suka ga dama iyayensu baza suce dan me ba,amma shi duk wannan bai damunsa,baima saka kansa cikin harkarsu,bai barin suzo gidansu saboda Dad ɗinsa ya nuna masa bai son yai making friends,mata kuwa idan ya ganshi da su yasan ranar ransa ne kawai Dad bazai zare ba,ba zai taɓa manta wata rana tun farko²n zuwansu da yake yaro,ya fita gidan ya tsaya waje,wata yarinya a neighbor's ɗinsu tazo tana masa magana tana faɗa masa sunanta da gidansu,kamar daga sama Dad ya fito ya gansu,bai masa magana ba kawai zuwa yai ya kama hannunshi,yana kallon Suzan yace kada ya sake ganinta tare da shi,bai ce masa ƙala ba sai da suka shiga gida,kamar zai cinyeshi saboda faɗa,tun daga ranan karatunshi ya koma akan kushe mata,duk hanyar da yasan zai cire masa tunanin ganin duk wani kyakkyawan hali akan mace,sai da yabi yai blackmail ɗin mace a zuciya da tunaninsa,shi ne abokinshi shi ne komai nasa a California,ɓangaren karatu ma shi yake masa a kwanakin weekends,duk abu mara kyau na lalata tarbiyya cikin hikima yake nuna masa,za ka sha mamaki idan kaga yanda Hamood ke ɗora ɗansa a hanya da bin diddigin duk abunda yake aikatawa,su wane irin friends yake tare da su,teachers ɗinsa a school ya ya suke? A rayuwarsa bai da buri bayan na son yaga ɗanshi ya fita daban,kuma shi kansa Wazeer yanda yaga Dad babu ruwansa da wasu mata,babu kowa cikin rayuwarsu daga su sai su,wannan ya bashi damar bin duk wasu footsteps na mahaifinsa,takatsan² yake da komai da kowa,idan ba dole ba babu abunda yake haɗashi magana da mata,a school seat ɗinsa kullum na front shi kaɗai,idan kana neman best student sunansa was the first ever da za kaji,shi yasa Hamood yake bala'in alfahari da shi,bai jin ƙyashin yai masa duk abunda yace yana so. A haka Wazeer ya kammala secondary School at age of 16,babu ɓata lokaci Hamood ya nemar masa gurbin karatu a Stanford University,nan ma dai Wazeer ya so cogewa,dan cewa yayi idan akwai makarantar da yake ba mix ba Dad ya nemar masa,Hamood yace "mene ne matsalarka ne?" Wazeer yace "nothing Dad but.." Hamood yace "tou babu.. Idan za kayi karatu kayi,mata ne ba dole sai ka shiga harkarsu ba,kayi abunda ya kaika ka gama,period.." Haka nan ya amsa,ya duƙufa abunda ke gabansa,ya fara karatunshi cikin tarin nasaraori inda yake ƙarantar abunda ya shafi marketing,bisa umarni da ra'ayin Dad ɗinsa,har kawo wannan lokacin su kaɗai suke ta rayuwa,tsakanin Hamood da gida da kowa sai dai a waya..

WAZEER!Where stories live. Discover now