ANYI GUDUN GARA PAGE 3

444 34 2
                                    

🌸🌸🌸💞💞💞🙆‍♀️
*ANYI GUDUN GARA*
🌸🌸🌸💞💞💞🙆‍♀️

         *NA*

        *AISHA*        
         *GALADIMA*

*DEDICATED TO*

*HASSAN ATKA*

*ALKHAIRIN ALLAH YA KAI GARE KU HAR GADON BACCI*

*MUM KHADY*
*RALEEYA*
*TEEMA DIMPLE*


*PG3*

  Ramla da sauri ta karaso wurin ta kama hannun Amal

Tana jijjigata ta na fadar "Amal baki dai ji ciwo ba ko" ?

Tuni hawaye sun fara anbaliya a fuskar Amal

A daidai lokacin khaleel ya kara so wurin be bi takan farouk bama ya matsa kusa da Ramla

"Bata ji ciwo ba ko?

"Eh ba ta ji ciwo ba"
Cewar Ramla

Ya mai da dubansa gun Amal  yace "kanwata Dan Allah ki dinga kallon gabanki idan kina kan titi ko hanya kin ji ko"
Ta daga masa kanta

Yace "good girl"
Sannan" kiyi hakuri da Marin da abokina ya miki ya ji
haushin abun da kika yi duk da be kyauta ba kinji

Ita dai Amal sheshshekar kukanta kawai take!

Ramla ce tace" ba komai mun gode ai laifinta ne da ta hau titi bata kallon gabanta "

Tuni farouk ya shige motar ya barsu nan tsaye

Koda khalel ya juyo se dai yaga wayam ya shige mota tafiya yyi shima ya shiga motar yana fadar "Amma dai gaskya farouk baka da kirki yarinyar da ka kusa turewa a mota ita ce har ka samu damar daga hannu ka mara"

Ko kulasa farouk be yi ba ya ja motar suka yi gaba...................

Amal kam ai har suka isa gida Tana kuka ga fuskar ta yi suntum abu ga farar fata sannan ga Marin da Tasha

Suna shiga ummah na fitowa da ga daki Ai ko Amal da gudu ta fada kanta Tana kuka!

Umma dagota tayi Tana "lafiya me ya same ki"?

Ai ko se ta Kara gunjin kukanta!
Se umma ta maida kallonta ga Ramla da ke cire sandal a kafarta

"Ke Ramla me ya sameta"?

Ramla tace"mota ce ta tashi kadeta tunda Kullum ita ce tafiya bata kallon gabanta ai ko me motar da kyar ma ya taka burki yana ko fitowa shine ya mareta "

Umma tureta tayi daga jikinta tace" wuce ki bani wuri dama wannan shashancin naki na in kina tafiya ba kya kallon gabanki baki Dena ba ko"?

"Ai ya min daidai dama Dan karan duka ya miki a hanyar gobe ki sake ki gani , wuce ki cire uniform kuyi sallah"

Da gudu ta shige daki Tana ci gaba da kukanta! ..........

¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶

To suma har suka je suka dawo duk maganar da khaleel yake masa share sa yayi , yana shigowa falonsa ya zube akan doguwar gujera yana lumshe idanunsa

Sautin karar wayarsa ne ya dawo dashi daga baccin da ya fara fizgarsa

Ganin Wanda yake kiransa yasa shi aza mar zauna wa tare da daukar wayar ya kara a kunne

"Assalamu Alaikum"
"Wa'alaikumu salamu" aka fada daga dayan bangaren
"Abbana ka wuni lafiya" cewar farouk

"Lafiya lau babana ya aikin naka"?
"Lafiya lau Abbah ya ummina da Al'ameen?

"Lafiya lau suke yaushe zaka zo gida ina son ganinka  tunda muna gari daya Amma ka koma zama barrack se ka kwana biyu ba mu saka a ido ba

"Insha'Allah yau gida zan kwana Abbana" ya kare maganar yana murmushi

"To yayi se ka zo

Waiwaye...............

Comments dinku shi ze kara min karfin gwiwa😀😀

ANYI GUDUN GARAWhere stories live. Discover now