Thirteen- Permanent Stalker

1.2K 207 33
                                    

Please don't forget to vote, comment and share with your friends.

Kwakwalwarsa tafasa yakeyi, komai ya cunkushe mashi. Banda jijiga Naseera baya komai. Tunanin yadda zaiyi masu Ardo bayanin abinda ya faru yakeyi. Kokuma abinda zai ce ma Dr Abdallah. Tabbas daga yau rayuwar sa zata canza.

Ruwa dake cikin buta a gefe ya gani, da sauri ya ɗauko ya soma watsa mata. Bata farka ba har lokacin. Aikam gaba ɗaya ya sheƙa mata shi. Nan ta soma jan numfashi tareda tari. Riko ta yayi da sauri saiya tallaba ta jikinsa. Bakinsa yana rawa ya soma magana.

"Naseera..."

Kallonsa ita kuma takeyi tarin ya tsagaita. Tana kokarin tuna abinda ya faru.

"Wallahi na sha..." sai yayi shiru baice Fauziyya ba. Tabbas yasan Naseera ta gaji da jin sunan Fauziyya a bakinsa.

"Nagode da kika farka, kiyi haƙuri in sha Allah bazan ƙara ba," yace tsoro ƙarara cikin idansa. Har lokacin jikinsa bai bar yin rawa na tashin hankali ba.

Ita bata amsa ba, binsa da kallo takeyi tana nazari. Jibe yanda ya susuce. Yayi kaca kaca kamar dambu. Sai kuma ta soma ɓanɓare kanta daga jikinsa. Batasan wani abu dazai haɗata dashi kwata kwata.

Shima ya lura saiya janye daga gareta, har lokacin bata bar kallonsa na al'ajabi ba. Anan sai taga cewa wata kila matsalar dake damunsa zai fi nata ta wani fanni. Domin duk tashin hankalin da take fuskanta idan ta kwanta barci baya hanata. Saidai idan ta tashi saita ɗaura daga inda ta tsaya.

Zuwa tayi wajen fitila zata sake kashewa tunda batasan silar shigan sa wannan yanayin ba kenan. Da sauri ya dakatar da ita.

"Kada ki kashe dan Allah," ya faɗa a tsorace. Binsa da kallo ta sake yi tana nazarin yanayin daya shiga. Kamar yaro ƙaramin ya koma.

Shimfidarta ta koma saita kwanta, barci da wuta a wajen yana takura mata. Amma ta tsinci kanta cikin kogin tausayin sa. Tabbas shima yanada nashi abin ruɗani. Anan ta tsinci kanta tana son sanin labarin sa. Ƙila idan taji nasa zataji dama dama akan abinda ke faruwa a nata.

Amma kuma data tuna cewa shine sanadin shigan ta nata matsalar. Sai kuma ta daina tausayin sa. Anan tayi mashi fatan Allah ya kawo mashi ruɗani ninkin ba ninkin. Kamar yadda bai koma barci ba haka itama bata koma ba. Itace ma taketa juye juye, shikam matashi yayi da hannunsa saiya kafa ma ceiling ido yayita kallo.

Baisan wanne yafi bashi takaici ba, rashin barcin sa koko shaƙe mutane idan sunzo kusa dashi. Kaico da lamarinsa yakeyi. Baisan ma ta inda zai fara ba domin yaji dama dama. Ya saba ganin turawa a film suna zuwa wajen therapist domin su samo masu mafita.

Amma baya ganin zai iya zuwa ofishin wata ya zauna yayita bayyana mata sirrin sa. Wani abu da sirri yanzu sai a fara maka kallo ana tausaya maka. Shi abinda ya tsana kenan. Gwara ka zage shi dakaji tausayin sa. Shi a ganinsa daga tausayi sai raini.

Dataga barcin ba mai zuwa bane saita fita tayi alwala, ya fiye mata zama tana tunane tunane, balle kuma datayi magana da Mahfooz gwara ayi mata duka da itace.

Anan tayita jero salloli, iyayenta taketa ma addu'a Idan tayi sujjada. Tabbas tasan suna cikin ruɗani musamman ummanta.

Da zakara yayi chara sai Ardo Bello ya fito, a lokacin shima Mahfooz ya fita. A wajensa yayi sallah. Bai koma ɗakin ba domin kwata kwata baya san yadda Naseera take tamke gira tamau. Abin yana bala'in ƙona mashi rai kamar zaiyi hauka amma yake dannewa.

Bayan kwana shida...

Haka rayuwa ya cigaba da kasance masu, basa shiga harkan juna kwata kwata. Abin yana bala'in ma Naseera daɗi kawai dai ita bata ganin gudun kwanakin ne. Idan taga Mahfooz toh daga nesa ne idan tazo wucewa. Shikam duk me tayi idansa yana kanta.

DIYAR DR ABDALLAH Where stories live. Discover now