Seventeen

1K 195 44
                                    

Ina wanda suka ce bazasu ƙara karanta ABDULQADIR ba? Kada Allah ya bako ikon yi. Sai meye idan baku karanta ba? Koko kuna tunanin cewa dan baku karanta ba zai cire mata wani abu daga cikin ruhinta? Koko kuna tunanin karatun ku shine iskar datake shaƙa kullum kuma rashin karatun ku zai ɗauke mata numfashi. Tun kafin a haifa mai sabulu balbela da farinta take. Dan rashin mutunci batayi maku komai ba sai ku bita private kuna zagin ta domin batayi update ba, wasu hakiman harda kiranta a waya suna zagi. Sannun ku Quraishawa dole ayi yadda kuke so. Her life revolves around you ai. Ita bazata yi ciwo ba, bazata je nema ba, bazata yi wasu hidama ba. Kawai zata zauna tayita feso maku da labari 24/7 idan kuma batayi ba sai ku soma tsine mata da makusanta ta. Ke idan kinada sabgar gabanki zaki ajiye karatu kije kiyi har wata sa'in fiye da sati guda, idan kin dawo kizo group kina cewa a tura maki wasu episodes saboda sanda aka tura you were busy ko bakida Lafiya. Amma writer bata isa tace tanada uzuri ba. Kuma the post she made on Wattpad SHE IS NOT SORRY. Wanda bazai iya jira ba sai yayi marabus da takardar yaje chan ya nema wanda aka gama ya karanta. Sannan kuma wasu na alakanta ta da wasu kungiya ana cewa bai kamata Lubna tayi update ɗin ba saboda ansan yan kungiyar basa haka, ana tunanin tanada hankali blah blah blah. Well bata cikin kowane kungiya, so apparently idan zaki zageta ki fito baro baro ki zageta as Lubna Sufyan. Da masu kuma cewa she's a writer bai kamata tayi post ɗin ba, zama da mutane saida haƙuri. You people are very selfish and heartless, watau writer ce kawai zatayi haƙuri. Ke da kike karatu ba zakiyi haƙuri ba? Kema ai alaƙa da mutane kike yi, so why won't you apply your theory on yourself? Wallahi Allah saiya saka mata, da masu zaginta, da masu mata sharri Allah saiya saka mata. Kunga shurun nan datayi maku kuna tunanin kun zaga banza? Wallahi zaku gani a gaba. Baku san uzurin ta ba, baku san ko tanada lafiya ba. Amma ku kawai a maku update, na tabbata ko gawarta kuka gani zaku riƙe kuce saiya karasa maku labari.

And please wanda zasu ce dama Ainau batada mutunci we expected more from her, don't worry I don't even care, never have and never will. So kwantar da hankalin ku. Kuma Lubna bazata yi rubutu ba sai randa ta samu ikon yi, mu makusanta ta munsan zafinta. And those clout chasers su cigaba da amfani da sunanta Allah ya basu sa'a. Wanda yaji haushin abinda nace ya hau dutsen kufena ya faɗo. Mind you, come at me and I'll drag your ancestors through hot coal and steel.

***

Haka Inna tayita kallon Rumasa'u tana mamaki, ai talauci ba hauka bane. Idan bata kunyar hulɗa dasu bai kamata ta ce sun mutu ba. Sai tayi marabus dasu kamar yadda tayi tun asali.

“Inna wallahi ba abinda kike tsammani bane,” tace idanta fal da hawaye. Itama ko ba'a faɗa mata ba tasan bata kyauta ba. Amma idan batayi haka ba Latisha bazata gane ita ba babban yarinya bace kuma zata yanke ta'ammali da ita. Inna bata ce komai ba, dama mayafi zata ɗauka domin ta kai markade, haka taje ta dawo.

Kallon Rumasa'u takeyi, irin kallon ƙurilla. Bata ce mata komai ba amma Rumasa'u ta gwammace datayi mata maganar data saba. Shirun yana takura mata, gaba daya ilahirin jikinta yayi sanyi duk bata jin daɗin.

Data fita zata je banɗaki, sai Inna tayi maza ta share hawayen dayake malalo mata. Tunda Rumasa'u take bata taɓa damuwa da abinda take saka iyayenta ba. Babu ruwanta, ita dai su biya mata buƙuta. Amma ta lura soyayyar ta yana cikin ran Inna. Koda take gidansu Rahina wata rana suna dawowa daga gantali tareda yan kungiyar One Love, sai taga Inna a layin. Tasan kuma tazo taji lafiyar ta ne, dayake direban yayi mankas. Saura kaɗan ya kwashe Inna da mota. Da kyar tasha daga kaidin sa.

“Ke tsohuwa dalla matsa,” ya daka mata tsawa mai firgitarwa. Yanda ta firgice abin dariya ne. Haka su Kankana suka bushe da dariya. Bata nuna masu cewa mahaifiyar ta bane kafin su raina mata wayo. Balle kayan jikinta ya koɗe duk yasha omo.

Ita Inna Nafisa tunani takeyi akan Rumasa'u, halinta sak yana kamada na yar uwanta Fauziyya. Kamar an tsaga kara. Mugun halinsu na kyaman talaka iri ɗaya, da Rumasa'u da Fauziyya batasan waye yake da dama daman zama ba.

DIYAR DR ABDALLAH Where stories live. Discover now