Humairah 3

8.4K 802 33
                                    

Tsakanin gidan Yasaiyadi da gidan Mr Ojo akwai tazara sosai, amma haka na tafi a kafa ni kadai, gashi dare yayi dan haka na ringa tafiya ina jin tsoro amma burina daya shine in je gurin mamana, I didn't even care anymore akan me Ojo zaiyi min. Ina zuwa unguwar na je har gate nayi knocking kaina tsaye, mai gadi ya bude ya tsaya yana kallona sai kuma ya kira wani Musty, Musty abokine kuma babban yaron Ojo yana yawan zuwa gidan ya sanni na san shi duk kuwa da cewa ba kula shi nake ba ko yayi min magana. Yana zuwa sai naga yayi sauri ya kama ni ya shiga dani dakin maigadi ya fara tambayata mai ya dawo dani gidan "what brought you back here, since you managed to escape why did you returned? Mr Daniel have got people out searching for you, he is really pissed up that a small girl has injured him this much, he had to get stitches and will forever have a scar on his forehead. No body can do that to Ojo and get away with it. You run away but your poor mother took the fall" Nan take yawun bakina ya kafe, I was counting on son da Ojo yake yiwa Mama ba zai barshi ya yi mata wani abu ba"

Humairah ta rufe fuska da hannayenta ta fara wani irin kuka mai ratsa zuciyar mai sauraro. Al'ameen kuwa in kaga idonsa zaka iya dauka garwashin wuta ne ba ido ba, sosai kukan Humairah yake shiga har cikin bargon sa amma kuma ya kasa rarrashinta, to me zaice mata? Sorry? Me sorry zata yi mata. All he wanted a lokacin was to take her in his arms and wipe away her tears amma babu dama tunda ba muharramarsa bace ba.

Sai da tayi kukanta mai isarta sannan ta cigaba da magana. "He told me cewa Ojo ya kashe mamana bayan ta dawo gida, he said 'she kept screaming your name har ta mutu'. I didn't shed a single tear, I was beyond crying amma naki yarda da abinda ya gaya min, I kept insisting cewa karya yake yi, nace ya kaini gurin ojo ya gaya min da bakinsa cewa ya kashe mamana, kuma su nuna min gawar tata in gani. Yaki kaini gurin ojo telling me cewa he was protecting me saboda yasan indai ojo ya ganni to karshe na kenan, amma ni lokacin bana tsoron mutuwar kuma, menene amfanin rayuwata in babu mamana? Me zan dauka a rayuwar gaba dayanta? Bai kaini gurin ojo ba amma sai ya kaini wani daki, dakin da tun da nazo gidan nasan ba'a bude shi kuma nasan abinda akeyi a dakin ba abu ne mai kyau ba. I saw her clothes, kayan da ta saka jiya da yamma, kayan dana ganta last dasu a jikinta, sucked in blood, her shoes and ear rings, duk da jini a jikinsu. Na tsaya kawai ina kallon kayan sannan na juya nace da musty "me yayi mata?"abinda yace min kawai shine "he gave her the most terrible death possible".

A bakin gate na tsaya nayi wa gidan kallon karshe, na kalli part din da muka zauna sai naga kamar zanga Mama ta leko tana kirana kamar yadda take yi duk sanda na fito waje, amma bata nan, she is gone, gone not only from the house but from the world. Musty ya sakani a motarsa, yace zai kaini gidansa sannan zai taimaka min wajan bincikar dangina. Hakan daya fada shi yasa na bishi saboda bani da burin daya wuce inga 'yan uwana. Gidansa can karshen garine, irin unguwar nan ce da yawanci guest houses ne a unguwar babu mutane sosai, muna zuwa ya bude min gidan muka shiga ya kaini wani daki ya bude na shiga sannan ya tsaya a bakin kofa yana kallona, sai kawai naga ya fara murmushi yace " kinsan me yasa na kawo ki gidana? Bawai taimaka miki zanyi ba karya nake yi, na dauko kine saboda bana so ojo ya kashe ki dan ina son in more ki. From now on, you are my little sex slave" sannan ya tsara min in details irin abubuwan da yake so inke yi masa, yace "we will start when you are ready" ya mayar da kofar ya rufe yayi tafiyarsa, ina jinsa ya rufe gate din gidan ya tafi. I screamed, I cried, I thought I was loosing my mind. Na rasa mahaifiyata sannan na rasa 'yancina a rana daya. Na yi blaming kaina for trusting Musty, na tuna maganar Mama da tace never trust a man, babu wanda zai taimaka miki don Allah sai don suna son wani abu daga gare ki.

Kullum Musty zai zo, kullum zaizo da daddare ya nemi in bashi abinda yake so ni kuma sai in zazzage shi da duk irin zagin dana iya, yace shi ba zai raping dina ba saboda baiga joy in raping ba, ya fi son duk abinda zanyi masa inyi masa willingly ni kuma naki. Azabar da yake min shine ta kadainci, ko palo ban taba fitowa ba kuma ni kadai ce a gidan dan in banda kukan tsuntsaye bana jin komai, daga baya kuma sai ya hada min da yunwa, da yakan kawo min abinci da daddare amma daga baya sai ya daina yace sai na amince dashi tukunna. Kwana na biyu babu abinci sai ruwa da nake sha daga pampon toilet. I thought I was dying amma kuma wani barin na zuciyata baya son mutuwar, so nake in rayu inga dangina, maybe ma inga babana.

Aisha_HumairahWhere stories live. Discover now