Page 3

303 27 1
                                    

    Bayan sun idar da sallah ne ikram ta d'akko mata wasu hotunan na bikin ta da bata gani ba.

     "Yaya kalleki a nan". Ikram ta nuna wani pic da Reyhana ta rife idanunta.

     Dariya dukansu sukai suka cigaba da kalla.Misalin 'karfe 7:08pm Inno ta gama abinci lokacin Abba suna parlour shida Ahmad suna 'yar hira.

     Bayan an kawo wa Ahmad abincin Abba ya tashi domin ya bashi waje dan ya kula ya kasa sake wa.Reyhana kuwa a d'aki suka ci tare da Ikram.

       Sageer shima lokacin ya shigo ,hannu ya mi'kawa Ahmad suka gaisa." Sageer ya school?" Ahmad ya tamabaya.

     "Alhamdulillah,kun shigo kenan?"

     "Eh d'azunnan". Ya amsa.

     " Ok,bari na watsa ruwa ". Sageer ya fad'a.

       D'akinsa ya wuce ,Reyhana kuwa ta shantake kamar bazata tafi ba hira ta'ki 'karewa.
  
      Koda ya gama yana zaune shi kad'ai a parlour sega kuma Sageer harya fito.D'an hira suka soma yi har lokacin isha'i yayi.Suna dawowa daga masjid yayiwa Reyhana text.

    " Toh Azizaty se a fito dare yana yi"
       
      Tana gama karancewa ta kalli agogo taga 8:13pm,nan take ta sauya fuska dan ji take kamar karta tafi sosai tayi kewar gida.

     "Ya de?" Ikram ta tambaya dan ta lura da chanjin fuskarta.

       "Ya Ahmad ne wai na fito mu tafi". Ta amsata.

       " Ayya! Yaya amaryar Ahmad ".Ikram ta fad'a cikeda tsokana.

      " Zan doke ki Ikram". Reyhana ta fad'a.

      "Sorry sister nice fa".

      " Toh ni ba wannan ba,yaushe zaki zo ki yinammin?"

       "Au wuni kad'ai zaki gayyaceni watoh banda kwana koh?" Ikram ta fad'a tana kallon Reyhana.

        "Ke dallah idan kwananma nace ai 'bata bakina zanyi". Ta fad'a.

       " InshaAllah zanzo bada dad'ewa ba yaya, yanzu de muje parlourn kar ya Ahmad yaji shiru". Ta fad'a.

     Parlour suka sauka se kuma suka iske Mommy ma tana parlourn gefe Abba da alama shiya kirata ta sakko da bazata zo siyi sallama ba."Reyhana kun fito kenan". Abba ya fad'a.

     "Eh". Ta amsa sanda ta 'karaso.

      " Sageer ashe ka dawo?" Cewar Reyhana.

       "Eh tun d'azu ,kina d'aki kunata hirarku". Ya amsata.

       " Toh ya school? "

       "Alhamdulillah". Ya amsa.

         Abba ne ya bawa Sageer key d'in motarsa yace akaisu gida,Mommy kuwa ta'be baki tayi taso yace akaisu a tata da anga tsiya.A haka sukai sallama itade Mommy fuskarta ba sakewa.

    Har 'kofar gida Sageer ya kaisu ,bayan sunyi sallama ya juya.Koda suka shiga gida ba light shiyasa da wuri suka kwanta tunda dama sunci abinci a gida.

                 ***

  Washegari 7:20am Ahmad ya gama shirinsa har breakfast ma ya kammala."Yau me za'a dafa da rana?"Reyhana ta tambayesa.

          " Ni duk abinda kika dafa yayi". Ya amsata yana zira takalmi.

         "OK dear seka dawo toh". Ta fad'a tare da mi'ka masa hularsa.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now