Page 35

407 23 6
                                    

    Not edited

Bayan kwana biyu Zainab ta dawo,jikinta a yanzu ya fara sanyi da auren wannan karan ko fad'a masu batai ba zata dawo kawai ganinta Umma tayi.

Shi Ahmad yana aiki daga nan d'in ma seya biya gidansu Reyhana tukun ze komo gida.Tunda tayi tafiya Zaria befi sau uku sukai waya ba satinta d'aya a can.

°°°
Reyhana tana jin sanda ya shigo parlour amma bata sauka 'kasa ba se Nasreen ce taje.Koda ya kirata 'kin picking tayi har ya tafi bata sakko ba.

Tana zaune Nasreen ta shigo tana murna hannunta ri'ke da leda "Uncle ya bani". Ta fad'a tana nuna mata.

" Toh naji ". Reyhana ta fad'a.

Kayan ciye-ciye ne kala-kala ya siyo mata.

•••

Koda ya koma gida d'akinsa ya shige besan ma Zainab ta dawo ba.

Yana zaune sega kiran Imran." Aboki yane?" Cewar Imran.

"Ya kua". Ahmad ya fad'a.

" Da matsala ne?" Ya tambaya.

"Kaima ka sani ai"Ahmad ya fad'a.

" Reyhanan de?"

"Ehyi ita".Ya amsa.

" Kaima ka bari se bayan wannan auren tukun ".

" For how long?"

"Duk yanda ya kai mana, kai da ka ha'kura da Zainab d'inka ma". Imran ya fad'a.

" Kai baza ka gane ba,tunda mike dake na ta'ba ce maka ina son Zainab? Imran nifa bana son yarinyarnan kawai de saboda Umma shiyasa zan ha'kura". Ahmad ya fad'a.

Zainab duk wannan zancen dayake yi a kunnenta ,tana tsaye jikin 'kofar d'akin sa.Umma ce ta sata kira mata shi ,zuwan da tayi ta riskeshi yana waya kunnenta ya jiyo mata wannan maganar.

Gwiwoyinta sinyi mata li'kis da 'kyar ta iya komawa d'akinta.Kuka mara sauti ta zauna ta shiga yi ba 'ka'k'kautawa.

"For all this long dama Ahmad be ta'ba sonta ba ,so Umma ce tasa ze aureta ashe ? Shiyasa baya nuna damuwa dani ". Abinda take fad'a a ranta kenan.

Umma jin shiru yasa ta biyo sawu ,Zainab na hango tahowar Umma tayi saurin goge hawayen ta.

" Zainab, naji shiru koh baya nan?" Ta tambaya.

"Yana.. yana zuwa". Ta fad'a.

Gid'a kai tayi tukun Umma ta fita ta koma d'akinta. Zainab sake goge fuskarta tayi sannan ta fita taje ta kira shi ,sam bata nuna alamar wani abu ba kuma shima be gano hakan ba.

D'akinta ta koma ta shiga wani sabon kukan ,tana son Ahmad sosai ba 'karamin ciwo abin yai mata ba duk wannan abun da take ashe shirmenta take,bata ga amfanin auren wanda bata so ba.Ta fad'a a ranta.

***
Sameer yau da yamma yazo gidansu Reyhana, da kanta ta kira shi tace tana so siyi magana a ranta ta gama yanke shawarar fad'a masa zata aureshi.

Bayan yazo sun gaisa da Mommy ta tashi ta bar musu parlourn Nasreen dama bata dawo daga school ba.

Bayan sun gaisa Reyhana tayi gyaran murya kafin ta soma magana.

"Ahma..uh..Sameer". Ta kira sunansa shaf ta mance ta kira shi da Ahmad.

" Dama ina so na fad'a maka shawarar da na yanke,uhn..Sameer na..."Be bari ta 'karasa ba ya katse ta.

"Reyhana base kinyi bayani ba na gano abinda kike so kice,na dad'e da fahimtar hakan ni kaina tun sanda naga Ahmad.."

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now