Page 20

212 16 4
                                    

    Alhamdulillah we reach page 20,happy page twenty🎈🎈   Umeeyr tace "Zainab want to snatch our ya Ahmad " 😂
Juma'at Kareem.

     Reyhana kwance a kan gado ,Nasreen na manne da jikinta ta zagaye hannunta a bayanta da hannin damanta na hagunta kuma tana shafa mata gashin kanta,Nasreen da tayi nisa da bacci hankalinta kwance.

       Babu rana da zata wuce Reyhana batayi tunanin Ahmad ba,idan ta tuna shekarun da aka shafe basu sake had'uwa ba kuma ba waya seta ji haushinsa wani 'bangaren zuciyarta kuwa har yanzu da gurbin sa a ciki."Meyasa ze guji 'yarsa? Mey Nasreen tayi masa a duniyannan daya watsar da ita?" Abinda kullum take tambayar kanta wanda amsar hakan ta gagara.

       Bata yi aune ba taji danshi a fuskarta,hannun ta sa da goge hawayen ,the more tana gogewa the more yana sake fitowa dan haka ta dena mah,gam ta sake ri'ke Nasreen a jikinta tare da d'ora ha'barta lightly a goshinta ,idonta ta rufe gam ba jimawa bacci yai gaba da ita.

                 ***

    Zainab 8am ta tashi dan bata fiya bacci dayawa ba bayan subh,kamar kullum a nitse tayi shara ba tare da Umma ta tashi ba,haka toilet ma ta wanke sannan ta koma d'aki.

       8:20am,wayarta dake jone a charge ta zare.Chat da sukai da Ahmad jiya ta shiga dubawa a hankali step by step tana sake karantawa tana murmushin.

       Data tayi switching on ko zata ganshi online,koda ta duba taga be hau ba tun jiyan.

       Tana jiyo fitowar Umma daga d'aki ta ajje wayar ta fita,cikin rissinawa ta gaisheta.

      "Zainab da sassafennan kika tashi harda shara".Cewar Umma.

      Murmushi kawai tayi ba tare da tace komai ba." To sannunki da 'k'o'kari".Umma ta fad'a.

       Har abincin breakfast tare sukai da ita,ko wanke-wanken ma bata bari Umma tayi ba ,haka Umma tayi ta shima ta albarka halin Zainab yana birgeta.

            ***
    Kiran Sameer ne yau ya tashi Reyhana 8:47am taji 'karar wayarta.

      "Hello". Ta fad'a bayan ta d'aga muryarta a cushe.

       " Morning ". Ya fad'a.

       " Morning ". Ta amsa rai a 'bace.

      " Tun d'azu nake jiran 9 yayi sena kira ki amma  I can't even wait,just want to know how you're doing ". Ya fad'a.

      " Am ok". Ta amsa kamar ta sha'ke shi.

     "Nasreen fah is she awake?" Ya tambaya.

      "Ya Allah". Ta furta a ranta dan ta gaji da amsasa ,magana da safe aiki yake mata haka kurum ma balle da Sameer.

       " Bata tashi ba nima bacci nake". Ta fad'a.

      "Oh am sorry na tashe ki,I just can't wait to hear your voice"

        "Uhmm". Ta fad'a.

        " Ok mayi waya anjima,yanzu ki koma bacci kinji bye". Ya fad'a.

         Ko amsasa batai ba tayi hanging taja tsuka.Baccin ma se ha'kura tayi.

      Tun kafin ta 'karasa sakkowa take jin hayaniyar su  Sageer.
  
        "Ku kuma kun cikawa mutane kunne daga tashi". Ta fad'a bayan ta sakko.

         "Hira muke me dad'i". Cewar Ikram.

         " Ni rufen baki". Ta fad'a tare da nufa kitchen.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now