Page 22

170 17 1
                                    

      Ahmad tun sanda sukai chat da Zainab be sake hawa online ba yau sati d'aya.Yana so yayi avoiding d'inta yana mey tsoron kar maganar Imran ta tabbata,d'azunma yana ganin kiranta amma ya'ki picking.

       Littafinsa ya d'auko ya soma karatu su Imran sun fita shi kad'ai ne a gidan.Kiran Umma ne ya shigo wayarsa,da farko yayi tunanin koh Zainab ce seya share,se a kira na biyu ya duba yaga Umma.
  
        "Umma ina kwana". Ya gaisheta.

        " Lafiya lau,ya karatu?"Umma ta tambaya.

        "Alhamdulillah". Ya amsa.

         " D'azu muka dawo daga asibiti Zainab bata da lafiya". Umma ta fad'a.

         " Toh! Meya sameta?"Ya tambaya.

         "Malaria neh". Ta amsa.

          " Allah ya sawwa'ke".Ya fad'a.

          "Ameen". Ta amsa sannan sukai sallama.

      " Shiyasa ta kirani ashe,Allah sarki".Ya fad'a a ransa.

     Dialing number d'inta yayi amma batai picking ba kusan 3× dole ya ha'kura a ransa ya ayyana ko fushi tayi tunda taga ya amsa kiran Umma.

      Karatunsa ya cigaba dayi se bayan 1hr tukun ya sake kiranta ,se a karo na biyu ta d'aga.

      "Assalamu Alaykum"

       "Waalaikumussalam". Ta amsa a hankali.

        " Zainab ".Ya kira sunanta.

         " Uhm".Ta amsa a ciki.

          "Ya jiki?" Ya tambaya.

           "Naji sau'ki". Ta amsa.

   Sunfi 2min ba wanda ya sake cewa komai.

       " Am sorry d'azu bana kusa da wayar lokacin da kika kira".Ahmad ya daure ya fad'a.

       "Uhm na gane".Ta fad'a.

        " Kinsha magani?" Ya tambaya yana so ya chanja topic.

      "Eh nasha". Ta amsa.

      " Toh ki daure ki dinga cin abinci kinji".

       "Tahm". Ta fad'a.

       Daga haka sukai sallama,ta ajje wayarta befi 1min ba message ya shigo.

    " Get well soon Sis"

     Lokaci guda ta saki murmushi ,har cikin ranta taji dad'i ya damu da ita.

                 ***
     Reyhana ce a d'aki ta ciga tayi fam haushin ya isheta saboda Abba yayi mata zancen Sameer.

      Mahaifiyar Sameer da kanta tazo wajen Mommy sukai maganar Reyhana Mommy kuma ta fad'a wa Abba abinda yake faruwa.

     Tana cikin wannan yanayin Walida ta shigo take fad'a mata Sameer yazo.

      "Kije kice ganinan".Reyhana ta fad'a.
   
      Mayafi ta d'auka ta yafa sannan ta fita.

      A falo ta tarar dashi shi kad'ai ko Nasreen bata nan,zama tayi opposite dashi.

       Bayan sun gaisa Sameer ya fara magana"Uh..Reyhana bakya ganin it's the right time?".

      " Right time for what?" Ta tambaya.

        "To give me chance, Reyhana baza kice bakisan abinda ke raina ba   duk iya tsahon shekarunnan ,at first nayi losing and now ga second chance na sake samu i don't want to miss it you know ,I so much care about your life,  everything yours you are always in my mind ,my love for you  will never vanish from my heart you are the only one i ever loved,  you are my first love and no woman can ever take your place in my heart, yet I never find someone like you  ,Reyhana you are different from others, you are unique, if am to stay here for years I can't stop describing how i valued you and the love that I have for you,Reyhana please consider".

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now