Page 23

152 18 1
                                    

   Did you see the pic above??👆

Washegari da safe around 8:15am kowa ya hallara a dining seat d'in Walida ne kad'ai empty se Nasreen da tun d'azu driver ya kaita makaranta.

   

"Walida bata tashi bane?" Abba ya tambaya.

"Ta tashi". Ikram ta amsa.

" Toh mey take baza ta fito ba?" Mommy ta fad'a.

"Ikram kije ki kirata". Cewar Mommy.

" Mommy nafa makara is almost 8:30am".Ikram ta fad'a.

"Bari na kirata". Reyhana ta fad'a tare da mi'kewa.

Murya taji 'kasa-'kasa lokacin da ta shiga d'akin,blanket taga alaman Walida ta rufe kanta dashi.

" My Prince ka daure kasha magani idan ba haka ba kanka ze cigaba da ciwone kaji".

Baki Reyhana ta saki jin muryar Walida tana waya.'Karasawa gadon tayi ta cukuikui blanket d'in ta yaye ta.

       Cikin razana Walida ta mi'ke zaune ,wayar ma tayi cilli gefe da ita,a zatonta Mommy ce.Ganin Reyhana ce yasa ta d'an ji relief tasan komai zezo da sau'ki
    
       "Iyye abinda kikeyi kenan?" Reyhana ta fad'a.

     Walida a sukwane ta d'auki wayar tayi hanging sannan ta dawo da kallonta wajen Reyhana.

       "Da 'kawata fa nake waya". Walida ta fad'a.

        " Shiyasa naji kina cewa My Prince ko? Ke bazaki nutsu ba koh ? Shikenan zan fad'a wa Abba kinga se ya aurar dake kowa ya huta naga alamar aure kike so".

       "Yaya dan Allah kiyi ha'kuri bazan 'kara ba". Walida ta fad'a.

       "Waye wannan d'in?" Reyhana ta tambaya.

        "Waseem". Ta amsa tana sosa kai.

         " A ina yake?"
        
          "Uhm..uhh d'an school d'inmu". Ta amsa a kunyace.

          " Class mate d'inki?,'karya yake miki wannan iyayensa ba aure zasi masa yanzu ba har nawa yake,just wannan year d'in fa kukai graduating kuma shine kike kulashi sakarya ,duk sanda na sake gani kina waya dashi sena fad'a wa Abba ya miki auren dole".

       Shiru tayi kanta a sunkuye ta'ki cewa 'kus.

     "Tashi ki wuce ki breakfast". Ta fad'a tare da ficewa.

      Bayanta tabi suka sauka 'kasa lokacin har Ikram ta tafi aiki.Muzurai tayi tayi kar Reyhana ta fad'a wa Mommy.

            ***

     Ahmad yau ko breakfast beyi ba ya fice a motarsa marcedes mey black color, yana hanya sega kiran Zainab.

        " Yaya ina kwana". Ta gaisheshi.

         "Lafiya lau". Ya amsa.

          " Umma tace gobe zaki dawo koh?"

           "Eh".Ta amsa.

            " Ok toh Allah ya kaimu".Ya fad'a ta amsa da Ameen ,daga haka sukai sallama ba tare da sunyi doguwar hira ba.

°°°

   3pm Reyhana da Mommy suna zaune a falo kamar daga sama suka ji an turo 'kofa da 'karfi.

     Sageer suka gani da sauri ya wuce d'akinsa ko ta kansu bebi ba.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now