Page 19

174 16 2
                                    

        "Ya Ahmad ina kwana".Aka fad'a daga d'ayan 'bangaren.

         " Lafiya lau".Ya amsa yana so yayi recognizing muryar me magana.

            "Zainab ce". Ta fad'a.

             " Oh! Zainab, ban d'auki muryar ba ya gida?" Ya tamabaya.

              "Lafiya lau,ya karatu?" Ta tamabaya.

              "Alhamdulillah". Ya amsa.

              " Ina gidan Umma fah".Ta sanar masa.

             "Ok ,kuna hutu ne??" Ya tambaya.

              "Uhh ai mun kammala ma". Ta amsasa.

        " Good,Allah yasa albarka". Ya fad'a.

           "Ameen,ga Umma zakui magana". Ta fad'a.

         " Ok bani ita".

        Umma da take kusa da ita ta mi'ka mata.

        "Ahmad kaji wayata shiru koh?" Cewar Umma bayan ta ma'kala a kunnenta.

        "Eh na kira bana saminki". Ya amsa.

         " Wayar ce ta samu matsala shine nasa Zainab ta kira ka ,tazo nan gida dayake ta samu admission a B.U.K  zata fara zuwa".Umma ta fad'a.

     "Ok,yanzu take fad'a mini sunyi graduation ashe har ta samu admission". Cewar Ahmad.

      " Ehh,na sami mey taya ni zama".Umma ta fad'a.

        "Gaskiya kam,zan kira sadiq seya kai maki gyaran wayar taki".

        Hira kad'an suka ta'ba sannan sukai sallama.

                ***
     Ta 'bangaren su Reyhana kuwa Inno ta tafi garinsu anyi rasuwa,yau kowa daya tashi seya nufo dining yaga wayam.

        " Mommy kuwa ta fito?" Reyhana ta tambayi bassam da yake falo shida Walida suna kallo.

       Bassam a shekaru ukunnan ya 'kara girma sosai dan ya kere Reyhana a tsaho yana 18yrs a yanzu,Walida ma ta 'kara tsaho se siranta kamar a 'balla ta😂

       "A'a". Suka amsata.

       " Tohh! 9am fah,kace yau za'a sha yunwa kuwa".Reyhana ta fad'a tare da shiga kitchen d'in.

      Ruwan tea ta d'ora a tea pot ta komo falo tai joining d'insu.

     Ba jimawa Mommy ta sakko."Ina kwana ".Suka gaisheta a tare.

      " Lafiya".Ta amsa had'e da yin hamma.

     "Bade baku d'ora wani abu ba?" Mommy ta tambaya.

      "Ina fa,yanzu kowa yake tashi". Reyhana ta amsa.

      " Aiko yau kowa ya d'and'ana inno kunsan bata nan nima yau hutawa zanyi kwasan yadda kukai".Mommy ta fad'a.

    "Nide na d'ora tea,Ikram da Walida kuyi saura". Reyhana ta fad'a.

      Ikram tana bacci Walida ta taso ta se turo baki take ita batason aiki.

       Sageer yana fitowa daga d'akinsa yaji kiran Reyhana, sasu tayi a gaba har bassam suka shiga kitchen Mommy tai zamanta a falo.

      " Oya jeki d'ebo dankali keda Walida zaku fere"Reyhana ta fad'a.

      Sageer shi dariya ma abin ya bashi saurayi dashi wai za'a had'a da girki.Gefe guda ya tsaya ya nad'e hannunsa  yana kallan ikon Allah ,jira yake yaga shi kuma nashi aikin.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now