Page 29

188 18 0
                                    

  Sageer bayan kamar 30min ya farka,lokacinda suka shiga be bari ya had'a ido dasu ba ya kawar da kansa.

         Dukkansu suna tunanin wannan wata damuwa ce ke damun Sageer data saka shi ya shiga cikin wannan halin banda Reyhana da ita tasan komai.

                    ***
      Around 3pm bayan ya dawo gida ya tarar da Sadiq,yana parlor suna hira da Umma.Ahmad suna gaisawa ya koma d'akinsa seda ya watsa ruwa tukun ya fito zuwa parlor lokacin Umma bata ciki.

     "Abokina yane?" Cewar Sadiq.

     Daga yadda yayi magana ya gano d'aya daga cikin rashin mutunci ne irin na Sadiq yasan Umma ta zayyane masa komai.

       Banza yayi masa bece komai ba sema wayarsa daya d'akko yana tapping.

      "Yanzu sede naji magana a wajen Umma instead ka same ni ka fad'a mini da kanka?" Sadiq ya fad'a.

       "Ni nasan ma mey kake nufi". Ahmad ya fad'a yana cigaba da danna wayarsa.

      " Zaka gane neh  na Zainab ".Sadiq ya fad'a yana 'kare maganar da dariya.

       " Kai! zan zageka".Cewar Ahmad wannan karan ba waya  yake kalla ba.
   
      "Seda kar a kuma, bani labari mana mey kake shirya mana neh?"

       "Bansani ba".Ahmad ya fad'a.

       " Munafiki kana so kana kaiwa kasuwa ,kayi ka gama".Sadiq ya fad'a.

       "Base ka ganni ba zakai". Ahmad ya fad'a yana mi'kewa yabar d'akin.

       " Ina kuma zaka ,koh ka manta zaka d'akko Zainab".Ya jiyo Umma ta fad'a.

        "Nima ze ragen hanya" Sadiq ya fad'a yana daga parlor.

       "Toh kaji". Umma ta fad'a.

      Ahmad a cukule ya fita banda Sadiq daya biyo shi yana sake 'kular dashi.Dama ba wani rage hanya dan har school dashi aka je d'akko Zainab se bayan suna hanyar dawowa ya sauka.

        Ko shiga gida Ahmad beyi ba ya tafi makarantar su Nasreen ,seda ya tsaya yayi mata siya-siye.

       •••

    Sageer kwanansu biyu a asibiti aka sallamesu har yanzu be fad'a musu abinda ke damunsa ba.Se bayan sun dawo gida Mommy ta titsiye Reyhana dan taga alamar akwai abinda take 'boyewa.

        "Mommy wata yarinya fa yake so shine iyayenta suka 'ki ,su cousin d'inta suke son su bata". Reyhana ta fad'a.

       " Yanzu dama akan haka ya shiga wannan halin !?"Cewar Mommy.

       "Tun yaushe akai hakan baku fad'a ba?" Ta tambaya.

        "An d'an dad'e". Ta amsa.

        " Yayi kyau da 'boye-'boye ga result nan ai kungani ze kashe kansa akan wata yarinya ".

        Mommy d'akin Abba taje ta zayyane masa komai, shi fad'a yayi tayi." Akan wata soyayya yana nema ya samu shiga cikin wani yanayi sakarai kawai".

       Har d'akinsa Abba yaje, Mommy tana tsayar dashi amma ko sauraronta beyi ba.

        "Kai yanzu dama wannan abun ne yake damunka kabi ka wahalar da mutane!?"

        Sageer daya sunkuyar dakai ko 'kala ya'ki fad'a yana jin Abba yana fad'a.

       "Karka fasa damuwar tunda a kanka aka fara soyayya baban soyayya kaji".Abba ya fad'a tare da ficewa.

ARZI'KI RABO(Completed)Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang