Page 17

197 21 5
                                    

     Safar  da take hannunta ta Nasreen ta saki a 'kasa,kukan ma ta kasa.

     "Ahmad ya sakeni?" Abinda take ta nanatawa kamar zautacciya.

     Kuka mara sauti ta soma,ita kuwa Nasreen se wuri wuri da ido take tana d'aga 'kafafuwa sama.

       Ahmad kuwa daga gidansu Reyhana gidansa ya koma yai zaman dirshan ,hotunan bikinsu ya d'auko yana ta kalla harda murmushin yake.

      Umma tayi tsammanin dawowarsa amma taji shiru,da ta kira wayarsa a kashe taji dan kuwa baya son jin kowa komai kawai yafison ya zauna shi kad'ai.

      Mommy da maghrib bayan tayi sallah ta shiga d'akin Reyhana lokacin tana toilet.Har zata fita ta hangi takardar a kan gado.

    A hankali ta 'karasa ta d'auka,koda ta karanta wani sanyi taji ya ratsa ta a zuciyarta tace"Alhamdulillah,an rabu da 'kaya".

      Hannunta ri'ke da takardar Reyhana ta fito fuskarta ba annuri da ka ganta za kasan tana cikin damuwa.

      Mommy ita kanta rasa abinda zata ce mata tayi dan tasan a wannan lokacin tana tare da 'bacin rai saboda haka Mommy ta ajje takardar ta fice.

         Abba kuwa da ya dawo Mommy ko kunya haka ta shiga d'akinsa ta sanar masa.

      "Toh yanzu hankalinki ya kwanta koh?" Abba ya fad'a
  
       Mommy shiru tayi bata ce komai ba se turo baki datai a zuciyarta kuwa tana mey jin dad'i.

           Ahmad se wajen 10:30am tukun ya koma gidan Umma da hankalinta ya tashi.

          "Kai kuwa ina ka shiga ina kiranka a kashe wayar?" Umma ta tambaya.

          "Naje gida neh". Ya amsa ciki ciki.

          " Du ka tayar min da hankali". Umma ta fad'a.

         "Kiyi ha'kuri". Ahmad ya fad'a.

           " Abinci fa?" Ta tambaya.

           "Na 'koshi ". Ya amsa ya shige d'aki.

        Kai kawai ta girgiza ta koma d'aki.

       Daren ranar daga Reyhana har Ahmad ba wanda ya iya bacci,daga ya fara gyangyad'i seyai mafarkin Reyhana tana kuka a firgice yake tashi.

                   ***

2weeks later

       Mommy itada Anty Asma'u sukaje gidan Ahmad suka sa aka kwaso kayanta ,dama kud'in hayar ya kusan 'karewa dan haka suna kwashe kayansu Ahmad ya dan'kawa mey gida gidansa.Shi kuwa ya komo gidan Umma.

        9:46pm yana rigingine ya 'kurawa ceiling ido yana tuna last maganar da sukai da Reyhana a waya.

  ** Waiwaye**

     
       " Reyhana am so sorry, I have no choice ".

        " Yaya na fahimta,stop apologizing ".Reyhana ta fad'a.

        "Wannan itace 'kaddararmu". Ahmad ya fad'a.

            Da'kyar ya iya rintse idonsa ba isashshen bacci yake ba yanzu.

            Mommy kuwa abin Reyhana ya fara isarta tun sanda Ahmad ya bata takardar ta ta dena sakin fuska ,fitowa parlour ma wataran se a wuni bata fito ba.

       Tana gyara gado dan shirin kwanciya Mommy ta shiga d'akin.

       Waje ta samu ta zauna,bayan data d'auki Nasreen da har lokacin idonta biyu.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now