Page 4

255 29 2
                                    

    Barka da juma'a  to all  Muslims💞

  Da asuba bayan ya dawo daga masjid Reyhana ta kai masa ruwan wanka toilet.

       Da kanta ta za'ba masa kayan sawa yana fitowa ya gansu ta ajje a kan gado ,T-shirt ce dark blue da ba'kin jeans ,da sauri ya saka ya shirya tsaf tukun ya fito.A kitchen ya taddata tana soya dankali.

      "Ina kwana". Ta gaisheshi.

       " Lafiya,ya bacci Azizaty jiya da wuri haka kika kwanta". Ahmad ya fad'a.
   
        "Eh toh naga kana ta marking". Ta fad'a.

           " Toh me ake dafa wa?" Ya tambaya.

           "Hmm dankali ne". Ta amsa.

           " Sannunki da 'ko'kari".

           "Yawwa dear". Ta amsa.

       Bayan mintina ta kammala ta kawo masa." Azizaty ke ba yanzu zaki ci ba?"

      "Se anjima".Ta amsa.

     Ba jimawa ya gama breakfast d'in,takalmi ta d'akko masa a d'aki yasa sannan ya tafi ,ita kuwa ta koma baccinta.

              ***

     Haka abubuwa suka cigaba da gudana ,Ikram da Walida sunzo sun wuni sageer ma yazo, Abba ne har yanzu daya cewa mommy suje seta ce ba yanzu ba ,sede yana waya da ita.

      Yau aurensu wata uku kenan,Reyhana na kitchen tana girki yau Saudat zata zo.

        " Azizaty 'kawar taki bata karaso ba kenan".Ahmad ya fad'a sanda ya fito tsakar gidan.

        "Minyi waya tace ta taho". Reyhana ta fad'a.

         " OK,bara zan d'an le'ka waje ba dad'ewa zan ba".Ya fad'a yana zira takalma.

         "Toh shikenan seka dawo".

        'Yan mintina 'kalilan ta 'karasa dama couscous da miyan ne se lemon cucumber tun jiya dama tayi mata cake ga exotic guda biyu daya ragu ta had'a mata da d'aya.

        2:45pm Saudat ta 'karaso gidan ,Reyhana tana d'aki tajiyo knocking d'inta da sauri taje ta bud'e."Besty!" Reyhana ta fad'a tare da hugging Saudat.

     "K'awas kai nayi  missing d'inki sosai sosai". Saudat ta fad'a.

      " Toh mu 'karasa ciki". Reyhana ta fad'a tare da breaking hug d'in.

        Sitting room tayi mata jagora suka 'karasa kowacce farinciki ya mamayeta."Amarya ashe zan sake ganinki".Cewar Saudat sanda suka zauna a kujera.

       "Ke d'ince koyaushe sa rana kin kasa zuwa,ya su Mama". Reyhana ta tamaya.

       " Duk lafiya suke,sunce a gaisheki".Saudat ta amsata.

        "Bari ina zuwa". Reyhana ta fad'a tare da fita.

         Abincin da sauran kayayyakin ta jero a tray ta kawo mata." Sakko ki ci se ai hirar".Cewar Reyhana.

          "Ohni Saudat du ni kad'ai".

          " Ehyi ke kad'ai.Ta amsa.

       Sakkowa tayi ta fara da,suna d'an hira tana ci."Ya Mommy kuwa tazo". Saudat ta tamabaya.

       "Ai Mommy har na fiddaran zuwanta har yanzu bata zo ba kuma Abba yana so zuzo amma shiru de,su Ikram de sunzo amma ko sisters d'in Mommy basu zo ba,na fad'a maki nifa bana ba'ki shiyasa kika ga ina azar'ba'bi kizo". Reyhana ta fad'a fuskarta na nuna tsantsar damuwa da hakan.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now