Page 13

188 20 0
                                    

      Washegari gajiyar da dama-dama sede Nasreen tasha bacci dan har lokacin bata farka ba.

      Har tayi wanka tayi breakfast Nasreen bata tashi ba,koda ta duba wayarta taga missed call na Ahmad ya kira tana bacci dan haka tayi calling ba.

      Kira d'aya tayi masa yayi picking.

       "Ummu Nasreen". Ahmad ya kira.

       "Abu Nasreen". Reyhana ta fad'a itama.

       " Ina kwana ".Ta gaisheshi.

       " Lafiya lao Azizaty,ya gajiyarku?"Ahmad ya amsa.

      "Gajiya ansha ta,har yanzu bacci take". Ta fad'a.

      "Allah sarki babyna du mutane sun wahalar min da ita".Ahmad ya fad'a.

      " Sannu mey baby".Reyhana ta fad'a cikin zolaya.

      "Ha! Toh ai gaskiya na fad'a". Cewar Ahmad yana dariya.

      " Toh nikuma fa banfita gajiya ba?" Reyhana ta fad'a.

     "Iyye! Kishi" Ahmad ya fad'a.

      "Haba kinsan da ina kusa da nayi maki tausa".Ahmad ya fad'a.

      " Nayi missing Azizaty ta ,your cooking pretty face everything yours Ummu Nasreen ".

      " Me too".Reyhana ta fad'a.

      "Toh yanzu kayi breakfast?" Ta tambaya.

      "Tea kawai nasha,yanzu zan fita ma". Ahmad ya fad'a.

      " Please ka samu kaci wani abun ko a wajen aikin ne".Cewar Reyhana tana mey nuna damuwa.

      "Ok Azizaty i will". Ya fad'a.

      " Toh bari na barka ka shirya".Ta fad'a.

      "Ok ki shafamin kan babyna i love you all". Ya fad'a.

     " Love you too,Allah ya kare mana kai".

     "Ameen". Ya amsa.

     Daga haka sukai sallama kowannensu fuskarsa d'auke da murmushi cikin ransu suna 'kara jin son junansu".

      Ba jimawa Nasreen ta tashi ,da kuka ta farka dan yunwa da take ji.Ta ded'e tana shan nono tukun aka yi mata wanka.

        Komai ya cigaba da gudana, Nasreen har bayan suna ana zuwa barka ga kayan gudumawa da ake bawa Reyhana yarinyar tayi goshi sosai banda kayan da Abba ya 'karo mata akan wanda su Umma suka kawo na barka.

        Ikram idan suna gida itace me d'aukan Nasreen Reyhana hutawarta take ,yarinyar ana ji da ita a gidannan Ahmad ma yana yawan zuwa baya kwana uku beje ba.

        Umma ma tana yawan kiransu su gaisa taji ya ta'kwararta.

      3weeks later,Ahmad yana ta irga musu kwanakinsu bashida buri su cika kwana 40 su dawo baya jin dad'in gidan kusan koyaushe yana unguwarsu wajen abokansa.

                  ***
      Mommy yau tai shirinta na zuwa gidan Anty Asma'u dan tunda Reyhana ta haihu bata samu ta fita ba.

         " Mommy dan Allah ku dawo da wuri saboda wankan Nasreen".Reyhana ta fad'a.

      "Yau ke zaki mata da kanki ai gara ki koya". Mommy ta fad'a.

       " Cabb! Kina so nasa mata sabulu a hanci". Reyhana ta fad'a.

      "Gaki gata kika samata kyasan yadda kikai". Mommy ta fad'a.

      Walida da tun tuni ta gama shiryawa Mommy take jira kawai su tafi.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now